ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Ɗalibai 6 A Kogi Bisa Zargin Kai Hari A Harabar Makaranta

by Rabi'u Ali Indabawa
2 months ago

Rundunar ƴansandan Jihar Kogi ta kama ɗalibai shida na Jami’ar Tarayya ta Lokoja bisa zargin aikata (bibiyar mutum ta Intanet da cin zarafi). Ɗaliban da aka kama sun haɗa da Inajo Henry, Nzekwe Ɓictor, Lucky Ɓictor, Lucky Gambo da Paul Daɓid, tare da wani mutum guda (yaro mai shekaru 17), dukkansu ɗalibai maza na Jami’ar Tarayya ta Lokoja.

A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, ASP Saliu Oyiza Afusat, ta fitar a ranar Talata, ta ce an kama su ne bayan wani ɗalibi namiji ya kai ƙorafi kan cin zarafi ta Intanet. Ta ce, “Rundunar ƴansandan Jihar Kogi na sanar da jama’a cewa a ranar 30 ga Maris, 2026, an kawo rahoton haɗa baki wajen aikata laifi, amfani da ƙarfi ba bisa ƙa’ida ba, ɓata suna, kai hari, da kuma cyberstalking a ofishin ‘B’ Diɓision, Lokoja, daga wani Oladosu Sunday, ɗalibi a Jami’ar Tarayya ta Lokoja.”

  • Wang Yi Ya Bukaci A Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Tattaunawa Tsakanin Mabambantan Wayewar Kai
  • 2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna
  • Bangaren Sin Ya Yi Kira Da a Dukufa Wajen Neman Mafita Ta Siyasa A Rikicin Ukraine
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’in Tsaro, Sun Yi Garkuwa Da Mutane Da Dama A Sokoto
  • Shugabannin Sin Da Koriya Ta Arewa Sun Sha Alwashin Wanzar Da Gagarumin Kawancen Gargajiya Tsakanin Kasashen Biyu

Ta ƙara da cewa daga baya aka miƙa shari’ar zuwa sashen binciken manyan laifuka na jiha domin gudanar da cikakken bincike cikin sirri.

ADVERTISEMENT

Bisa ga bayaninta, bayan bincike mai zurfi, rundunar ta kama waɗanda ake zargi: Inajo Henry, Nzekwe Ɓictor, Lucky Ɓictor, Lucky Gambo da Paul Daɓid, tare da wani yaro mai shekaru 17, dukkansu ɗalibai maza.

Ta ce binciken farko ya nuna cewa waɗanda ake zargin, ba tare da wata hujja mai inganci ba, sun zargi Oladosu Sunday da zama ɗan luwadi, sannan suka shirya yadda za su jawo shi zuwa gidansu da ke kusa da yankin Liɓing Faith Church a Felele, Lokoja, a ranar 29 ga Maris, 2026, da misalin ƙarfe 9:00 na dare.

LABARAI MASU NASABA

Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Gayyaci NSA da Ministoci Kan Yawaitar Satar Mutane

Sace Ɗalibai Ya Karu A Mulkin Tinubu Fiye Da Gwamnatocin Baya – Obi

An bayyana cewa sun ƙulle shi a cikin ɗaki, suka tuɓe masa kaya da ƙarfi, sannan suka yi masa mugun duka da bel da wayoyin caja, yayin da suke ɗaukar bidiyo.

Ta ce daga baya an yaɗa bidiyon a intanet, inda ya bazu a tsakanin ɗaliban jami’ar.

Ta ƙara da cewa waɗanda ake zargin sun amsa laifin yayin tambayoyi, inda suka ce sun shirya aikata hakan ne tun da farko bisa zargi marar tabbaci game da halayen wanda aka cutar.

Mai magana da yawun rundunar ta ce an kammala bincike, kuma an gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban kotun da ta dace.

Rundunar ta sake jaddada cewa ba za ta amince da ɗaukar doka a hannu, cin zarafi ta yanar gizo, ko duk wani nau’in laifi ba.

Ta gargaɗi jama’a, musamman matasa da ɗalibai, da su guji ɗaukar doka a hannu ko aikata ayyukan da ke take haƙƙin ɗan ‘Adam da mutuncin wasu, tare da shawartar masu ƙorafi da su bi hanyoyin doka wajen neman haƙƙinsu.

Ta tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da kare haƙƙin kowa da kuma tabbatar da hukunta masu laifi.

Kwamishinan ƴansandan jihar, Naziru Bello Kankarofi, ya tabbatar wa al’ummar Jihar Kogi ƙudirin rundunar na kare rayuka da dukiyoyi, tare da kira ga jama’a da su ci gaba da ba da haɗin kai wajen yaƙi da laifuka.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Da ‘Yan Sa-kai Sun Ceto Shanu 245 Da Aka Sace A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Daure Mutum Biyu Shekara 24 Saboda Kashe Wani Dan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

MASU ALAKA

Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Gayyaci NSA da Ministoci Kan Yawaitar Satar Mutane
Manyan Labarai

Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Gayyaci NSA da Ministoci Kan Yawaitar Satar Mutane

June 9, 2026
Sace Ɗalibai Ya Karu A Mulkin Tinubu Fiye Da Gwamnatocin Baya – Obi
Tsaro

Sace Ɗalibai Ya Karu A Mulkin Tinubu Fiye Da Gwamnatocin Baya – Obi

June 6, 2026
Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
Tsaro

Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

June 5, 2026
Next Post
Yawan Kuɗaɗen Da Ke Wajen Bankuna Sun Ragu Zuwa Kashi 3.66 A Watan Fabrairu

Yawan Kuɗaɗen Da Ke Wajen Bankuna Sun Ragu Zuwa Kashi 3.66 A Watan Fabrairu

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi Ya Bukaci A Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Tattaunawa Tsakanin Mabambantan Wayewar Kai

Wang Yi Ya Bukaci A Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Tattaunawa Tsakanin Mabambantan Wayewar Kai

June 9, 2026
ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam’iyya

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

June 9, 2026
Bangaren Sin Ya Yi Kira Da a Dukufa Wajen Neman Mafita Ta Siyasa A Rikicin Ukraine

Bangaren Sin Ya Yi Kira Da a Dukufa Wajen Neman Mafita Ta Siyasa A Rikicin Ukraine

June 9, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’in Tsaro, Sun Yi Garkuwa Da Mutane Da Dama A Sokoto

June 9, 2026
Shugabannin Sin Da Koriya Ta Arewa Sun Sha Alwashin Wanzar Da Gagarumin Kawancen Gargajiya Tsakanin Kasashen Biyu

Shugabannin Sin Da Koriya Ta Arewa Sun Sha Alwashin Wanzar Da Gagarumin Kawancen Gargajiya Tsakanin Kasashen Biyu

June 9, 2026
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nemi A Haramta Shigo Da Yadiddika Domin Farfaɗo da Masaƙun Cikin Gida

June 9, 2026
Xi: An Cimma Matsayar Raya Dangantakar Sin Da Koriya ta Arewa A Sabon Zamani

Xi: An Cimma Matsayar Raya Dangantakar Sin Da Koriya ta Arewa A Sabon Zamani

June 9, 2026
Kwankwaso

A Shirye Nake In Sasanta Da Gwamnan Kano – Kwankwaso

June 9, 2026
Sin Ba Za Ta Kyale Japan Da Philippines Su Take Hakkokinta Na Ruwa Ba

Sin Ba Za Ta Kyale Japan Da Philippines Su Take Hakkokinta Na Ruwa Ba

June 9, 2026
Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Gayyaci NSA da Ministoci Kan Yawaitar Satar Mutane

Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Gayyaci NSA da Ministoci Kan Yawaitar Satar Mutane

June 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.