ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Ɗalibai 6 A Kogi Bisa Zargin Kai Hari A Harabar Makaranta

by Rabi'u Ali Indabawa
3 months ago

Rundunar ƴansandan Jihar Kogi ta kama ɗalibai shida na Jami’ar Tarayya ta Lokoja bisa zargin aikata (bibiyar mutum ta Intanet da cin zarafi). Ɗaliban da aka kama sun haɗa da Inajo Henry, Nzekwe Ɓictor, Lucky Ɓictor, Lucky Gambo da Paul Daɓid, tare da wani mutum guda (yaro mai shekaru 17), dukkansu ɗalibai maza na Jami’ar Tarayya ta Lokoja.

A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, ASP Saliu Oyiza Afusat, ta fitar a ranar Talata, ta ce an kama su ne bayan wani ɗalibi namiji ya kai ƙorafi kan cin zarafi ta Intanet. Ta ce, “Rundunar ƴansandan Jihar Kogi na sanar da jama’a cewa a ranar 30 ga Maris, 2026, an kawo rahoton haɗa baki wajen aikata laifi, amfani da ƙarfi ba bisa ƙa’ida ba, ɓata suna, kai hari, da kuma cyberstalking a ofishin ‘B’ Diɓision, Lokoja, daga wani Oladosu Sunday, ɗalibi a Jami’ar Tarayya ta Lokoja.”

  • Na Tsaya Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
  • Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma
  • “Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka
  • Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

Ta ƙara da cewa daga baya aka miƙa shari’ar zuwa sashen binciken manyan laifuka na jiha domin gudanar da cikakken bincike cikin sirri.

ADVERTISEMENT

Bisa ga bayaninta, bayan bincike mai zurfi, rundunar ta kama waɗanda ake zargi: Inajo Henry, Nzekwe Ɓictor, Lucky Ɓictor, Lucky Gambo da Paul Daɓid, tare da wani yaro mai shekaru 17, dukkansu ɗalibai maza.

Ta ce binciken farko ya nuna cewa waɗanda ake zargin, ba tare da wata hujja mai inganci ba, sun zargi Oladosu Sunday da zama ɗan luwadi, sannan suka shirya yadda za su jawo shi zuwa gidansu da ke kusa da yankin Liɓing Faith Church a Felele, Lokoja, a ranar 29 ga Maris, 2026, da misalin ƙarfe 9:00 na dare.

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

An bayyana cewa sun ƙulle shi a cikin ɗaki, suka tuɓe masa kaya da ƙarfi, sannan suka yi masa mugun duka da bel da wayoyin caja, yayin da suke ɗaukar bidiyo.

Ta ce daga baya an yaɗa bidiyon a intanet, inda ya bazu a tsakanin ɗaliban jami’ar.

Ta ƙara da cewa waɗanda ake zargin sun amsa laifin yayin tambayoyi, inda suka ce sun shirya aikata hakan ne tun da farko bisa zargi marar tabbaci game da halayen wanda aka cutar.

Mai magana da yawun rundunar ta ce an kammala bincike, kuma an gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban kotun da ta dace.

Rundunar ta sake jaddada cewa ba za ta amince da ɗaukar doka a hannu, cin zarafi ta yanar gizo, ko duk wani nau’in laifi ba.

Ta gargaɗi jama’a, musamman matasa da ɗalibai, da su guji ɗaukar doka a hannu ko aikata ayyukan da ke take haƙƙin ɗan ‘Adam da mutuncin wasu, tare da shawartar masu ƙorafi da su bi hanyoyin doka wajen neman haƙƙinsu.

Ta tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da kare haƙƙin kowa da kuma tabbatar da hukunta masu laifi.

Kwamishinan ƴansandan jihar, Naziru Bello Kankarofi, ya tabbatar wa al’ummar Jihar Kogi ƙudirin rundunar na kare rayuka da dukiyoyi, tare da kira ga jama’a da su ci gaba da ba da haɗin kai wajen yaƙi da laifuka.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tsaro

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

July 11, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’
Tsaro

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Next Post
Yawan Kuɗaɗen Da Ke Wajen Bankuna Sun Ragu Zuwa Kashi 3.66 A Watan Fabrairu

Yawan Kuɗaɗen Da Ke Wajen Bankuna Sun Ragu Zuwa Kashi 3.66 A Watan Fabrairu

LABARAI MASU NASABA

Na Tsaya Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Tsaya Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026
Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

July 13, 2026
Jiragen Kasan Sin Sun Yi Tafiye-Tafiyen Fasinjoji Sama Da Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Jiragen Kasan Sin Sun Yi Tafiye-Tafiyen Fasinjoji Sama Da Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.