ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Ɗalibai 6 A Kogi Bisa Zargin Kai Hari A Harabar Makaranta

by Rabi'u Ali Indabawa
2 months ago

Rundunar ƴansandan Jihar Kogi ta kama ɗalibai shida na Jami’ar Tarayya ta Lokoja bisa zargin aikata (bibiyar mutum ta Intanet da cin zarafi). Ɗaliban da aka kama sun haɗa da Inajo Henry, Nzekwe Ɓictor, Lucky Ɓictor, Lucky Gambo da Paul Daɓid, tare da wani mutum guda (yaro mai shekaru 17), dukkansu ɗalibai maza na Jami’ar Tarayya ta Lokoja.

A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, ASP Saliu Oyiza Afusat, ta fitar a ranar Talata, ta ce an kama su ne bayan wani ɗalibi namiji ya kai ƙorafi kan cin zarafi ta Intanet. Ta ce, “Rundunar ƴansandan Jihar Kogi na sanar da jama’a cewa a ranar 30 ga Maris, 2026, an kawo rahoton haɗa baki wajen aikata laifi, amfani da ƙarfi ba bisa ƙa’ida ba, ɓata suna, kai hari, da kuma cyberstalking a ofishin ‘B’ Diɓision, Lokoja, daga wani Oladosu Sunday, ɗalibi a Jami’ar Tarayya ta Lokoja.”

  • An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
  • Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
  • Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Ta ƙara da cewa daga baya aka miƙa shari’ar zuwa sashen binciken manyan laifuka na jiha domin gudanar da cikakken bincike cikin sirri.

ADVERTISEMENT

Bisa ga bayaninta, bayan bincike mai zurfi, rundunar ta kama waɗanda ake zargi: Inajo Henry, Nzekwe Ɓictor, Lucky Ɓictor, Lucky Gambo da Paul Daɓid, tare da wani yaro mai shekaru 17, dukkansu ɗalibai maza.

Ta ce binciken farko ya nuna cewa waɗanda ake zargin, ba tare da wata hujja mai inganci ba, sun zargi Oladosu Sunday da zama ɗan luwadi, sannan suka shirya yadda za su jawo shi zuwa gidansu da ke kusa da yankin Liɓing Faith Church a Felele, Lokoja, a ranar 29 ga Maris, 2026, da misalin ƙarfe 9:00 na dare.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

An bayyana cewa sun ƙulle shi a cikin ɗaki, suka tuɓe masa kaya da ƙarfi, sannan suka yi masa mugun duka da bel da wayoyin caja, yayin da suke ɗaukar bidiyo.

Ta ce daga baya an yaɗa bidiyon a intanet, inda ya bazu a tsakanin ɗaliban jami’ar.

Ta ƙara da cewa waɗanda ake zargin sun amsa laifin yayin tambayoyi, inda suka ce sun shirya aikata hakan ne tun da farko bisa zargi marar tabbaci game da halayen wanda aka cutar.

Mai magana da yawun rundunar ta ce an kammala bincike, kuma an gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban kotun da ta dace.

Rundunar ta sake jaddada cewa ba za ta amince da ɗaukar doka a hannu, cin zarafi ta yanar gizo, ko duk wani nau’in laifi ba.

Ta gargaɗi jama’a, musamman matasa da ɗalibai, da su guji ɗaukar doka a hannu ko aikata ayyukan da ke take haƙƙin ɗan ‘Adam da mutuncin wasu, tare da shawartar masu ƙorafi da su bi hanyoyin doka wajen neman haƙƙinsu.

Ta tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da kare haƙƙin kowa da kuma tabbatar da hukunta masu laifi.

Kwamishinan ƴansandan jihar, Naziru Bello Kankarofi, ya tabbatar wa al’ummar Jihar Kogi ƙudirin rundunar na kare rayuka da dukiyoyi, tare da kira ga jama’a da su ci gaba da ba da haɗin kai wajen yaƙi da laifuka.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi
Tsaro

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

June 19, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Manyan Labarai

Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano

June 17, 2026
Next Post
Yawan Kuɗaɗen Da Ke Wajen Bankuna Sun Ragu Zuwa Kashi 3.66 A Watan Fabrairu

Yawan Kuɗaɗen Da Ke Wajen Bankuna Sun Ragu Zuwa Kashi 3.66 A Watan Fabrairu

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.