Rundunar ƴansandan Jihar Kogi ta kama ɗalibai shida na Jami’ar Tarayya ta Lokoja bisa zargin aikata (bibiyar mutum ta Intanet da cin zarafi). Ɗaliban da aka kama sun haɗa da Inajo Henry, Nzekwe Ɓictor, Lucky Ɓictor, Lucky Gambo da Paul Daɓid, tare da wani mutum guda (yaro mai shekaru 17), dukkansu ɗalibai maza na Jami’ar Tarayya ta Lokoja.
A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, ASP Saliu Oyiza Afusat, ta fitar a ranar Talata, ta ce an kama su ne bayan wani ɗalibi namiji ya kai ƙorafi kan cin zarafi ta Intanet. Ta ce, “Rundunar ƴansandan Jihar Kogi na sanar da jama’a cewa a ranar 30 ga Maris, 2026, an kawo rahoton haɗa baki wajen aikata laifi, amfani da ƙarfi ba bisa ƙa’ida ba, ɓata suna, kai hari, da kuma cyberstalking a ofishin ‘B’ Diɓision, Lokoja, daga wani Oladosu Sunday, ɗalibi a Jami’ar Tarayya ta Lokoja.”
- Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
- Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
- Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
- ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP
- An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Ta ƙara da cewa daga baya aka miƙa shari’ar zuwa sashen binciken manyan laifuka na jiha domin gudanar da cikakken bincike cikin sirri.
Bisa ga bayaninta, bayan bincike mai zurfi, rundunar ta kama waɗanda ake zargi: Inajo Henry, Nzekwe Ɓictor, Lucky Ɓictor, Lucky Gambo da Paul Daɓid, tare da wani yaro mai shekaru 17, dukkansu ɗalibai maza.
Ta ce binciken farko ya nuna cewa waɗanda ake zargin, ba tare da wata hujja mai inganci ba, sun zargi Oladosu Sunday da zama ɗan luwadi, sannan suka shirya yadda za su jawo shi zuwa gidansu da ke kusa da yankin Liɓing Faith Church a Felele, Lokoja, a ranar 29 ga Maris, 2026, da misalin ƙarfe 9:00 na dare.
An bayyana cewa sun ƙulle shi a cikin ɗaki, suka tuɓe masa kaya da ƙarfi, sannan suka yi masa mugun duka da bel da wayoyin caja, yayin da suke ɗaukar bidiyo.
Ta ce daga baya an yaɗa bidiyon a intanet, inda ya bazu a tsakanin ɗaliban jami’ar.
Ta ƙara da cewa waɗanda ake zargin sun amsa laifin yayin tambayoyi, inda suka ce sun shirya aikata hakan ne tun da farko bisa zargi marar tabbaci game da halayen wanda aka cutar.
Mai magana da yawun rundunar ta ce an kammala bincike, kuma an gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban kotun da ta dace.
Rundunar ta sake jaddada cewa ba za ta amince da ɗaukar doka a hannu, cin zarafi ta yanar gizo, ko duk wani nau’in laifi ba.
Ta gargaɗi jama’a, musamman matasa da ɗalibai, da su guji ɗaukar doka a hannu ko aikata ayyukan da ke take haƙƙin ɗan ‘Adam da mutuncin wasu, tare da shawartar masu ƙorafi da su bi hanyoyin doka wajen neman haƙƙinsu.
Ta tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da kare haƙƙin kowa da kuma tabbatar da hukunta masu laifi.
Kwamishinan ƴansandan jihar, Naziru Bello Kankarofi, ya tabbatar wa al’ummar Jihar Kogi ƙudirin rundunar na kare rayuka da dukiyoyi, tare da kira ga jama’a da su ci gaba da ba da haɗin kai wajen yaƙi da laifuka.















Discussion about this post