Mutum hudu ne suka rasa rayukansu a harin tashin hankali da ya faru a kusa da Afor Market Junction a kauyen Nawfia, cikin Karamar Hukumar Njikoka, Jihar Anambra.
Jami’in Hulda da Jama’a na Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Anambra, SP Tochukwu Ikenga, ya tabbatar da haka a cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Litinin.
- EFCC Ta Kama Tsohon Gwamnan Anambra Chris Ngige A Abuja
- Ƴansanda Sun Zafafa Farautar Mambobin Ƙungiyar Asiri Ta ‘Sai Malam’ A Sakkwato
Ikenga ya ce harin ya samo asali ne daga rikicin kungiyoyin asiri masu hamayya da juna, yana mai karawa da cewa wasu daga cikin mambobin kungiyar daya, wadanda ke amfani da motar Black Ledus Jeep mai lambar da “ba a sani ba”, sun mamaye kasuwar Afor Nawfia suka harbe mutum ba tare da tantancewa ba.
Ya ce ‘yan ta’addan sun tsere kafin isowar ‘yansanda, amma bayanan farko da aka tattara a wurin sun bayar da muhimman bayanai, kuma Rundunar tana aiki a kai don tabbatar da an gano masu laifin kuma an kama su.
Sanarwar ta ce a wani bangare, “Rundunar ‘Yansanda ta Jihar Anambra na son bayar da cikakken bayani kan harin da ya shafi kungiyoyin asiri da ya faru a yammacin ranar 7 ga Disamba, 2025, a kasuwar Afor Nawfia, a kan tsohon titin Onitsha zuwa Awka.
“Idan za a iya tunawa cewa, kwanaki hudu kafin wannan lamari, jami’an rundunar da ke cikin Special Anti-Cult Skuad, Enugwu-Ukwu, bisa sahihan bayanai kan shirin rikicin kungiyoyin asiri masu hamayya, sun kama mutum biyu masu hadari kuma sun karbi bindiga daga gare su.
“Mutumn da aka kama suna ba ‘yansanda muhimmiyar bayanai domin hana wasu tashin hankali na kungiyoyin asiri a cikin Awka da kewaye. Duk da wadannan matakai na rigakafi da jami’an rundunar suka dauka, wani mamba daga wannan kungiyar guda daya, a yammacin ranar 7 ga Disamba, 2025, yana amfani da mota Black Ledus Jeep mai lamba da ba a sani ba, sun mamaye kasuwar Afor Nawfia suka harbi mutum.”
“Wannan harin tashin hankali ya yi sanadin mutuwar mutum hudu, bayan haka ‘yan ta’addan sun tsere daga wurin. Ko da yake sun tsere kafin isowar ‘yansanda, bayanan farko da aka tattara a wurin sun bayar da muhimmiyar jagora, kuma Rundunar tana aiki a kai don tabbatar da cewa an gano masu laifin kuma an kama su.”
Ya bayyana cewa Rundunar tana da kudurin kawar da kungiyoyin asiri, laifuka masu tashin hankali da duk wani nau’in laifi a jihar.
“Za a sanar da karin bayani yayin da bincike ke ci gaba,” in ji shi.
Majiyoyi daga yankin sun ce lamarin ya jawo rudani yayin da mutane suka yi ta tserewa domin neman tsira, tare da karawa da cewa wasu mutanen sun mutu har lahira sakamakon harbin bindiga.
Wata majiya ta ce, “‘Yan ta’addan da ke rike da makamai sun mamaye Afor Market Junction sannan nan da nan suka fara harbi, suka kashe mutane da yawa. Babu wanda ya san dalilin harin, amma lamarin ya girgiza al’ummarmu.”
Wasu mazauna da suka bayyana ra’ayinsu kan lamarin sun ce har yanzu suna cikin tashin hankali, inda da dama ke kiran a kara tsaro a yankin.
Wani shaida a kusa da wurin ya ce, “Halin da aka shiga gaskiya ya rikita mutane. Masu kai harin sun fito daga wurin da babu wanda ya sani a wannan yammacin suka fara harbin kaio mai uwa da wabi
“‘Yansanda sun kaddamar da bincike kan harin kuma suna aiki don kama masu laifin.”
Hotunan bidiyo na lamarin da ake yadawa a Intanet sun nuna mazauna suna gudu domin tsira, yayin da wasu gawawwaki ke kwance a cikin jini a kasa.














