ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe Mutum 4 A Rikicin ‘Yan Kungiyar Asiri A Anambra

by Rabi'u Ali Indabawa
6 months ago
Anambra

Mutum hudu ne suka rasa rayukansu a harin tashin hankali da ya faru a kusa da Afor Market Junction a kauyen Nawfia, cikin Karamar Hukumar Njikoka, Jihar Anambra.

Jami’in Hulda da Jama’a na Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Anambra, SP Tochukwu Ikenga, ya tabbatar da haka a cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Litinin.

  • EFCC Ta Kama Tsohon Gwamnan Anambra Chris Ngige A Abuja
  • Ƴansanda Sun Zafafa Farautar Mambobin Ƙungiyar Asiri Ta ‘Sai Malam’ A Sakkwato

Ikenga ya ce harin ya samo asali ne daga rikicin kungiyoyin asiri masu hamayya da juna, yana mai karawa da cewa wasu daga cikin mambobin kungiyar daya, wadanda ke amfani da motar Black Ledus Jeep mai lambar da “ba a sani ba”, sun mamaye kasuwar Afor Nawfia suka harbe mutum ba tare da tantancewa ba.

ADVERTISEMENT

Ya ce ‘yan ta’addan sun tsere kafin isowar ‘yansanda, amma bayanan farko da aka tattara a wurin sun bayar da muhimman bayanai, kuma Rundunar tana aiki a kai don tabbatar da an gano masu laifin kuma an kama su.

Sanarwar ta ce a wani bangare, “Rundunar ‘Yansanda ta Jihar Anambra na son bayar da cikakken bayani kan harin da ya shafi kungiyoyin asiri da ya faru a yammacin ranar 7 ga Disamba, 2025, a kasuwar Afor Nawfia, a kan tsohon titin Onitsha zuwa Awka.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

“Idan za a iya tunawa cewa, kwanaki hudu kafin wannan lamari, jami’an rundunar da ke cikin Special Anti-Cult Skuad, Enugwu-Ukwu, bisa sahihan bayanai kan shirin rikicin kungiyoyin asiri masu hamayya, sun kama mutum biyu masu hadari kuma sun karbi bindiga daga gare su.

“Mutumn da aka kama suna ba ‘yansanda muhimmiyar bayanai domin hana wasu tashin hankali na kungiyoyin asiri a cikin Awka da kewaye. Duk da wadannan matakai na rigakafi da jami’an rundunar suka dauka, wani mamba daga wannan kungiyar guda daya, a yammacin ranar 7 ga Disamba, 2025, yana amfani da mota Black Ledus Jeep mai lamba da ba a sani ba, sun mamaye kasuwar Afor Nawfia suka harbi mutum.”

“Wannan harin tashin hankali ya yi sanadin mutuwar mutum hudu, bayan haka ‘yan ta’addan sun tsere daga wurin. Ko da yake sun tsere kafin isowar ‘yansanda, bayanan farko da aka tattara a wurin sun bayar da muhimmiyar jagora, kuma Rundunar tana aiki a kai don tabbatar da cewa an gano masu laifin kuma an kama su.”

Ya bayyana cewa Rundunar tana da kudurin kawar da kungiyoyin asiri, laifuka masu tashin hankali da duk wani nau’in laifi a jihar.

“Za a sanar da karin bayani yayin da bincike ke ci gaba,” in ji shi.

Majiyoyi daga yankin sun ce lamarin ya jawo rudani yayin da mutane suka yi ta tserewa domin neman tsira, tare da karawa da cewa wasu mutanen sun mutu har lahira sakamakon harbin bindiga.

Wata majiya ta ce, “‘Yan ta’addan da ke rike da makamai sun mamaye Afor Market Junction sannan nan da nan suka fara harbi, suka kashe mutane da yawa. Babu wanda ya san dalilin harin, amma lamarin ya girgiza al’ummarmu.”

Wasu mazauna da suka bayyana ra’ayinsu kan lamarin sun ce har yanzu suna cikin tashin hankali, inda da dama ke kiran a kara tsaro a yankin.

Wani shaida a kusa da wurin ya ce, “Halin da aka shiga gaskiya ya rikita mutane. Masu kai harin sun fito daga wurin da babu wanda ya sani a wannan yammacin suka fara harbin kaio mai uwa da wabi

“‘Yansanda sun kaddamar da bincike kan harin kuma suna aiki don kama masu laifin.”

Hotunan bidiyo na lamarin da ake yadawa a Intanet sun nuna mazauna suna gudu domin tsira, yayin da wasu gawawwaki ke kwance a cikin jini a kasa.

Anambra
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Wakilin Musamman Na Shugaban Kasar Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Na Shekarar Zaman Lafiya Da Aminci A Turkmenistan

Wakilin Musamman Na Shugaban Kasar Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Na Shekarar Zaman Lafiya Da Aminci A Turkmenistan

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.