ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe Mutum 4 A Rikicin ‘Yan Kungiyar Asiri A Anambra

by Rabi'u Ali Indabawa
7 months ago
Anambra

Mutum hudu ne suka rasa rayukansu a harin tashin hankali da ya faru a kusa da Afor Market Junction a kauyen Nawfia, cikin Karamar Hukumar Njikoka, Jihar Anambra.

Jami’in Hulda da Jama’a na Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Anambra, SP Tochukwu Ikenga, ya tabbatar da haka a cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Litinin.

  • EFCC Ta Kama Tsohon Gwamnan Anambra Chris Ngige A Abuja
  • Ƴansanda Sun Zafafa Farautar Mambobin Ƙungiyar Asiri Ta ‘Sai Malam’ A Sakkwato

Ikenga ya ce harin ya samo asali ne daga rikicin kungiyoyin asiri masu hamayya da juna, yana mai karawa da cewa wasu daga cikin mambobin kungiyar daya, wadanda ke amfani da motar Black Ledus Jeep mai lambar da “ba a sani ba”, sun mamaye kasuwar Afor Nawfia suka harbe mutum ba tare da tantancewa ba.

ADVERTISEMENT

Ya ce ‘yan ta’addan sun tsere kafin isowar ‘yansanda, amma bayanan farko da aka tattara a wurin sun bayar da muhimman bayanai, kuma Rundunar tana aiki a kai don tabbatar da an gano masu laifin kuma an kama su.

Sanarwar ta ce a wani bangare, “Rundunar ‘Yansanda ta Jihar Anambra na son bayar da cikakken bayani kan harin da ya shafi kungiyoyin asiri da ya faru a yammacin ranar 7 ga Disamba, 2025, a kasuwar Afor Nawfia, a kan tsohon titin Onitsha zuwa Awka.

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

“Idan za a iya tunawa cewa, kwanaki hudu kafin wannan lamari, jami’an rundunar da ke cikin Special Anti-Cult Skuad, Enugwu-Ukwu, bisa sahihan bayanai kan shirin rikicin kungiyoyin asiri masu hamayya, sun kama mutum biyu masu hadari kuma sun karbi bindiga daga gare su.

“Mutumn da aka kama suna ba ‘yansanda muhimmiyar bayanai domin hana wasu tashin hankali na kungiyoyin asiri a cikin Awka da kewaye. Duk da wadannan matakai na rigakafi da jami’an rundunar suka dauka, wani mamba daga wannan kungiyar guda daya, a yammacin ranar 7 ga Disamba, 2025, yana amfani da mota Black Ledus Jeep mai lamba da ba a sani ba, sun mamaye kasuwar Afor Nawfia suka harbi mutum.”

“Wannan harin tashin hankali ya yi sanadin mutuwar mutum hudu, bayan haka ‘yan ta’addan sun tsere daga wurin. Ko da yake sun tsere kafin isowar ‘yansanda, bayanan farko da aka tattara a wurin sun bayar da muhimmiyar jagora, kuma Rundunar tana aiki a kai don tabbatar da cewa an gano masu laifin kuma an kama su.”

Ya bayyana cewa Rundunar tana da kudurin kawar da kungiyoyin asiri, laifuka masu tashin hankali da duk wani nau’in laifi a jihar.

“Za a sanar da karin bayani yayin da bincike ke ci gaba,” in ji shi.

Majiyoyi daga yankin sun ce lamarin ya jawo rudani yayin da mutane suka yi ta tserewa domin neman tsira, tare da karawa da cewa wasu mutanen sun mutu har lahira sakamakon harbin bindiga.

Wata majiya ta ce, “‘Yan ta’addan da ke rike da makamai sun mamaye Afor Market Junction sannan nan da nan suka fara harbi, suka kashe mutane da yawa. Babu wanda ya san dalilin harin, amma lamarin ya girgiza al’ummarmu.”

Wasu mazauna da suka bayyana ra’ayinsu kan lamarin sun ce har yanzu suna cikin tashin hankali, inda da dama ke kiran a kara tsaro a yankin.

Wani shaida a kusa da wurin ya ce, “Halin da aka shiga gaskiya ya rikita mutane. Masu kai harin sun fito daga wurin da babu wanda ya sani a wannan yammacin suka fara harbin kaio mai uwa da wabi

“‘Yansanda sun kaddamar da bincike kan harin kuma suna aiki don kama masu laifin.”

Hotunan bidiyo na lamarin da ake yadawa a Intanet sun nuna mazauna suna gudu domin tsira, yayin da wasu gawawwaki ke kwance a cikin jini a kasa.

Anambra
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Next Post
Wakilin Musamman Na Shugaban Kasar Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Na Shekarar Zaman Lafiya Da Aminci A Turkmenistan

Wakilin Musamman Na Shugaban Kasar Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Na Shekarar Zaman Lafiya Da Aminci A Turkmenistan

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.