ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe Wani Mutum Saboda Cajar Wayar Hannu A Anambra

by Leadership Hausa
5 months ago

An kashe wani matashi mai suna Chisom, sanadin fada akan cajar wayar hannu a Ihiala, Jihar Anambra.

PUNCH Metro ta samu labarin cewa lamarin ya faru ne a ranar 19 ga Disamba bayan wata takaddama tsakanin shi da dan uwansa wanda har yanzu ba a gano sunansa ba.

  • Harin Bam A Masallacin Borno Aiki Ne Na Rashin Imani — Ministan Sufuri
  • Jam’iyyar NNPP Za Ta Yi Gagarumin Tasiri A Zaben 2027 – Kwankwaso

A cewar wani rubutu da aka gani a dandalin wayar da kan jama’a kan yaki da kungiyoyin asiri, Confra Naija, a ranar Talata, Chisom ya taba bayar da cajin wayar ga dan uwansa a baya.

ADVERTISEMENT

Sai dai rikici ya barke lokacin da Chisom ya tafi daukar cajin wayar, wanda daga bisani ya rikide zuwa fada mai tsanani. A yayin wannan fada, an zargi dan uwansa da yankan Chisom wurare da dama.

Dandalin ya kara da cewa, mahaifin wanda ake zargi, wanda shi Baffan Chisom ne, kuma ya farmake shi, lamarin da ya kai ga mutuwar Chisom.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

Rubutun ya ce: “A Ihiala, wani matashi mai suna Chisom ya kashe shi dan uwansa wanda ba mamba ne na kungiyar asiri ba, saboda sabani kan cajin wayar hannu.”

“An ce Chisom ya ba dan uwansa cajin wayar, daga bisani sai ya tafi karba, amma rikici ya barke, inda dan uwansa ya yanke shi da wuka wasu wuarare da dama a yayin fadan.”

Dandalin ya kara da cewa an kama dan uwan nasa a baya, yayin da matasa a cikin al’umma suka kona gidan Baffan nasa.

A cikin wani bidiyo da wakilinmu ya gani, an ga gawar mamacin kwance a gadon asibiti yayin da ‘yan uwansa ke kuka.

Kokarin samun martani daga Jami’in Hulda da Jama’a na ‘Yansandan Jihar Anambra, Tochukwu Ikenga, bai yi nasara ba, saboda bai amsa kiran waya ba. kazalika bai amsa sakon kar-ta-kwana da aka tura masa ba ba har lokacin kammala wannan rahoto.

Takaddama tsakanin ‘yan uwa sau da yawa tana rikidewa zuwa tashin hankali mai kisa a wasu sassa na jihar. Wadannan sun hada da sabani kan kadarori, kudi, da sauran al’amuran sirri, wanda sau da yawa ke karewa da jini.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja
Kotu Da Ɗansanda

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

May 2, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

April 25, 2026
An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya

April 25, 2026
Next Post
Masana Sun Bayyana Yadda Kasafin Kudin 2026 Zai Shafi Tsaro Da Ilimi Da Kiwon Lafiya

Masana Sun Bayyana Yadda Kasafin Kudin 2026 Zai Shafi Tsaro Da Ilimi Da Kiwon Lafiya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.