ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jam’iyyar NNPP Za Ta Yi Gagarumin Tasiri A Zaben 2027 – Kwankwaso

by Leadership Hausa
9 months ago

A gabanin zabukan 2027, ‘dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a shekarar 2023, Sanata Rabiu Kwankwaso, ya yi alkawarin cewa jam’iyyar za ta yi gagarumin tasiri a lokacin zaben 2027.

A yayin da yake Magana da manema laarai a Abuja a taron kwamitin zartarwa na kasa na jam’iyya, Kwankwaso wanda shi ne jagoran kuma tsohon gwamnan Jihar Kano ya yaba da tsarin jam’iyyar da ayyukanta, yana mai cewa ita ce daya daga cikin jam’iyyun da suke da tasiri da yin aiki sosai a kasar nan.

  • Mutane 5 Sun Rasu, 35 Sun Jikkata A Harin Bam A Masallaci A Borno
  • Sarki Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Bayan Shafe kwana 25 A Hannun Masu Garkuwa A Kwara

Yayin da yake taya sabon shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Farfesa Joash Amupetan murna, ya nuna fata cewa zai yi nasara a aikinsa, Kwankwaso ya yaba wa mambobin jam’iyyar don gudanar da zabukan reshen jam’iyyar a fadin kasar cikin ladabi da tsari, yana mai cewa jam’iyyar ta shirya sosai don tunkarar zaben 2027.

ADVERTISEMENT

Ya kuma gode wa gwamnan Jihar Kano, Abba Yusuf, saboda goyon bayansa da kyakkyawan aiki, haka nan ya yi kira ga mambobin jam’iyya su ci gaba da zama masu himma da hadin kai, ya jaddada cewa hadin kai da fahimtar juna da jajircewa sune makullin nasarar jam’iyya.

Tun da farko a jawabinsa, shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dakta Ajuiji Ahmed wanda kuma ya samu nasarar yi tazarce na ci gaba da shugabancin jam’iyya, ya ce jam’iyyar ta tsaya tsayin daka duk da kokarin kawo cikas ga ayyukanta, amma hakan haskaka nasarorin jam’iyyar, inda ya jaddada shugabanci mai cike da hadin kai tsakanin mambobi, da kuma kokarin yin biyayya ga muhimman ka’idoji.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

Ya yaba wa gwamnan jam’iyyar a Jihar Kano saboda samar da abubuwan more rayuwa na ilimi da lafiya da gine-gine da ci gaban Dan’adam, yana mai cewa gwamnan ya daga tutar jam’iyyar sosai.

Ahmed wanda ya kuma ya ba wa jagoran jam’iyyar na kasa tare da siffanta shi a matsayin gwarzon siyasa a Kano da ma Nijeriya gaba daya. Ya yi kira ga mambobin jam’iyya su ci gaba da mayar da hankali kan manufofinsu, yana mai cewa jam’iyya na goyon bayan jaronta na kasa da gwamnanta wajen samun nasara a zaben 2027.

Ahmed ya kuma yi gargadi kan yunkurin tilasta wa Nijeriya ta koma tsarin jam’iyya daya, yana mai cewa irin wadannan kokarin zai kai ga ruguza kasar nan baki daya.

Maganganun shugaban NNPP sun zo ne a tsakiyar jita-jitar da ke yawo game da makomar jam’iyyar da rawar da take takawa a siyasar Nijeriya.

A cikin jawabinsa, sakataren jam’iyyar na kasa, Oladipo Olayuku, ya yaba wa shugabannin jam’iyyar ciki har da Sanata Rabiu Musa Kwankwasa da Gwamna Abba Kabir Yusuf, saboda rawar da suka taka wajen sauya fasali jam’iyyar wanda ta yi tasiri a kasa baki daya.

Olayuku ya cewa lokacin da shugaban jam’iyyar na yanzu ya karbi mulki a shekarar 2022, NNPP ba a san shi sosai ba, amma ta hanyar kokarinsu, ya zama sananne a ko’ina kuma jam’iyya ce ta kasa baki daya, kamar yadda ya yaba da yadda jam’iyyar ta yi a zaben 2023, duk da cin amanar da wasu ‘ya’yan jam’iyyar suka yi, kuma ya yaba da gwamnan Jihar Kano da sauran jami’an da aka zaba saboda kyakkyawan aikinsu.

Olayuku wanda ya yi godiya ga bangarenn shari’a saboda kin amfani da su wajen keta tsarin gudanarwar jam’iyya, ya bayyana cewa jam’iyyar ta sake duba kundin tsarinta, ta canza tambari da takenta da tutarta, kuma tana shirye-shirye tun karar zaben 2027.

Olayuku ya yi kira ga ‘ya’yan jam’iyya su yi aiki tare, su manta da batutuwan rashin jituwa, su kuma goyi bayan sabon shugabanci da za a bayyana a taron kasa na jam’iyyar.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
  • Leadership Hausa
    Batun Guguwar Kakar Yakin Neman Zabukan 2027 A Nijeriya

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Da Sahalewar Nijeriya Bayan Samun Bayanan Sirri Amurka Ta Kai Hari — Tuggar

Da Sahalewar Nijeriya Bayan Samun Bayanan Sirri Amurka Ta Kai Hari — Tuggar

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.