ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe ‘Yan Ta’adda 39, An kama 159 A Borno Da Yobe

by Abubakar Abba
2 years ago
Ta'adda

Sojin rundunar Operation Hadin Kai, sun yi wa wasu ‘yan bindiga kwanton bauna, wanda hakan ya ba su nasarar kashe 39 tare da kama 159 daga cikinsu. 

Kazalika, sojin sun kuma ceto mutane 109 da masu garkuwa suka sace a waje daban-daban.

  • Ana Zura Ido Kan Yadda Amurka Za Ta Ki Raba-gari Da Kasar Sin
  • Dan Daba Ya Yi Wa Dan Jarida Dukan Tsiya A Cikin Gidan Gwamnatin Adamawa

Daraktan yada labarai na rundunar tsaro Majo Janar Edward Buba, ya shaida wa manema labarai hakan a yau Alhamis shalkwatar rundunar da ke Abuja.

ADVERTISEMENT

Ya ce, rundunar sojin kasa, ta lashi tokobin ci gaba da dakile masu son yi wa kasar nan zagon kasa na samun ‘yanci.

Ya ci gaba da cewa, jirgin sojin sama ya yi luguden wuta a wani sansanin ‘yan bindiga a dajin Sububu da ke a karamar hukumar Kankara ta Jihar Katsina, inda suka tarwatsa sansanin nasu.

LABARAI MASU NASABA

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bugu da kari, ya ce sojin sun kuma yi wa wasu manyan ‘yan ta’addar Boko Haram da na ISWAP kwanton bauna, inda suka kama su, a Gwoza da Tarmuwa da ke a Borno da kuma Yobe.

A cewarsa, hakan ya kuma tilasta wasu daga cikin ‘yan ta’addar mika wuya a Gwoza da ke a jihar Borno, inda a wannan nasara, sojin suka kashe wasu ‘yan ta’addar suma kuma ceto mutanen da suka sace tare da kwato makamai da albarusai.

Bugu da kari, sojin a wani aikin da suka yi, sun hallaka ‘yan ta’adda 11, sun cafke 45 sun kuma ceto mutane 34, tare da kuma kwato makamai da albarusai.

Ya ce, daga cikin makaman sun hada da, bindigun AK-47 shida, bindiga daya kirar HK21, bindiga daya kirar GPMG, bindiga kirar gida guda daya, kunshin albarusai guda 11 da sauransu.

Ya ce, sojin rundunar Operation Safe Haven da ke aiki a Arewa ta Tsakiya, sun kashe ‘yan bindiga biyu sun kuma ceto mutane uku da aka sace tare da kuma kama ‘yan bindiga 15.

Kazalika, ya ce sojin rundunar Operation Delta Safe a mako biyun da suka gabata, sun kama wasu da ake zargin barayin mai ne a yankin Neja Delta da kuma mutane 34 da sarrafa haramtacciyar matatar mai, wadda sojin suka lalata.

Bugu da kari Buba ya sanar da sojin sun kuma dakile yunkurin masu satar mai, tare da kwace kudi Naira miliyan 765.8 a wajensu da kama makamai guda 55 da albarusai guda 96.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Next Post
Bukatar Samar Da Kariya Ta Musamman Ga Makarantunmu

Bukatar Samar Da Kariya Ta Musamman Ga Makarantunmu

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.