• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe ‘Yan Ta’adda 39, An kama 159 A Borno Da Yobe

by Abubakar Abba
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sojin rundunar Operation Hadin Kai, sun yi wa wasu ‘yan bindiga kwanton bauna, wanda hakan ya ba su nasarar kashe 39 tare da kama 159 daga cikinsu. 

Kazalika, sojin sun kuma ceto mutane 109 da masu garkuwa suka sace a waje daban-daban.

  • Ana Zura Ido Kan Yadda Amurka Za Ta Ki Raba-gari Da Kasar Sin
  • Dan Daba Ya Yi Wa Dan Jarida Dukan Tsiya A Cikin Gidan Gwamnatin Adamawa

Daraktan yada labarai na rundunar tsaro Majo Janar Edward Buba, ya shaida wa manema labarai hakan a yau Alhamis shalkwatar rundunar da ke Abuja.

Ya ce, rundunar sojin kasa, ta lashi tokobin ci gaba da dakile masu son yi wa kasar nan zagon kasa na samun ‘yanci.

Ya ci gaba da cewa, jirgin sojin sama ya yi luguden wuta a wani sansanin ‘yan bindiga a dajin Sububu da ke a karamar hukumar Kankara ta Jihar Katsina, inda suka tarwatsa sansanin nasu.

Labarai Masu Nasaba

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

Bugu da kari, ya ce sojin sun kuma yi wa wasu manyan ‘yan ta’addar Boko Haram da na ISWAP kwanton bauna, inda suka kama su, a Gwoza da Tarmuwa da ke a Borno da kuma Yobe.

A cewarsa, hakan ya kuma tilasta wasu daga cikin ‘yan ta’addar mika wuya a Gwoza da ke a jihar Borno, inda a wannan nasara, sojin suka kashe wasu ‘yan ta’addar suma kuma ceto mutanen da suka sace tare da kwato makamai da albarusai.

Bugu da kari, sojin a wani aikin da suka yi, sun hallaka ‘yan ta’adda 11, sun cafke 45 sun kuma ceto mutane 34, tare da kuma kwato makamai da albarusai.

Ya ce, daga cikin makaman sun hada da, bindigun AK-47 shida, bindiga daya kirar HK21, bindiga daya kirar GPMG, bindiga kirar gida guda daya, kunshin albarusai guda 11 da sauransu.

Ya ce, sojin rundunar Operation Safe Haven da ke aiki a Arewa ta Tsakiya, sun kashe ‘yan bindiga biyu sun kuma ceto mutane uku da aka sace tare da kuma kama ‘yan bindiga 15.

Kazalika, ya ce sojin rundunar Operation Delta Safe a mako biyun da suka gabata, sun kama wasu da ake zargin barayin mai ne a yankin Neja Delta da kuma mutane 34 da sarrafa haramtacciyar matatar mai, wadda sojin suka lalata.

Bugu da kari Buba ya sanar da sojin sun kuma dakile yunkurin masu satar mai, tare da kwace kudi Naira miliyan 765.8 a wajensu da kama makamai guda 55 da albarusai guda 96.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ta'addaBornoSojojiYobe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ana Zura Ido Kan Yadda Amurka Za Ta Ki Raba-gari Da Kasar Sin

Next Post

Bukatar Samar Da Kariya Ta Musamman Ga Makarantunmu

Related

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?
Manyan Labarai

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

2 hours ago
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

7 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

8 hours ago
Likitoci
Manyan Labarai

NARD Ta Janye Yajin Aikin GargaÉ—i Da Ta Fara

9 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

13 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

22 hours ago
Next Post
Bukatar Samar Da Kariya Ta Musamman Ga Makarantunmu

Bukatar Samar Da Kariya Ta Musamman Ga Makarantunmu

LABARAI MASU NASABA

Duba Ga KwaÉ—ayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

Duba Ga KwaÉ—ayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

September 14, 2025
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

September 14, 2025
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

September 14, 2025
Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

September 14, 2025
An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

September 14, 2025
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

September 14, 2025
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

September 14, 2025
Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

September 14, 2025
Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

September 14, 2025
Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.