ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Samar Da Kariya Ta Musamman Ga Makarantunmu

by Leadership Hausa
3 years ago
Kariya

A ‘yan shekaraun nan, Nijeriya ta ci gaba da fuskantar abubuwa marasa dadi na tashin hankali na hare-hare a makarantunmu, makarantu da ya kamata su kasance wuri na samar da matasan da za su zama jagororin al’umma a nan gaba, a yanzu sun zama wurare da ake zaune cikin tsoro da zullumi da tashin hankali.

A yayin da muke nazarin kididdgar da wata kungiya mai zaman kanta mai suna ‘Safe the Children’ ta fitar, ya zama dole a matsayinmu na kasa mu gaggauta samar da hanyoyin kare makarantunmu daga ayyukan masu garkuwa da mutane da ‘yan bindiga.

  • Ana Zura Ido Kan Yadda Amurka Za Ta Ki Raba-gari Da Kasar Sin
  • Dan Daba Ya Yi Wa Dan Jarida Dukan Tsiya A Cikin Gidan Gwamnatin Adamawa

Rahoton kungiyar ya nuna cewa, tun daga lokacin da aka sace ‘yan makarantan nan su 276 a garin Chibok da ke Jihar Borno a shekarar 2014, ‘yan makaranta fiye da 1,680 aka yi garkuwa da su. Wannan lamari na tayar da hankali, don kuwa ‘yan makaranta 180 suka rasa rayukansu yayin da 90 suka ji raunuka daban-daban a hare-haren da aka kai wa makarantu a fadin tarayyar Nijeriya abin da ya zama wata barazana da kuma tashin hankali ga sauran dalibai da iyayensu.

ADVERTISEMENT

Haka kuma, bayani ya nuna cewa, an yi garkuwa da malaman makarantu 60 yayin da malamai 14 suka rasa rayukansu a hare-haren da aka kai makarantun an kuma lalata makarantu 25 a sassan Nijeriya.

A matsayinmu na gidan jarida, ra’ayinmu a nan shi ne, wadannan ba wai suna matsayin kididdiga ba ne kawai sun zama wani lamari da ke dakushe  mafarkin matasanmu na zama wani abu a nan gaba, yana kuma lalata ginshiki da fatan da ake da shi ta bunkasar tsarin karatun Nijeriya gaba daya.

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

An kaddamar da wannan kungiyar ta ‘Safe Schools Initiatibes’ ce bayan da aka sace ‘yan matan makarantar Chibok a shekarar 2014 da mufin tabbatar da kariya ga makarantunmu. Wannan shiri yana samun tallafi da goyon bayan Majalisar Dinkin Duniya, da kungiyar ‘yan kasuwan Nijeriya da sauran kungiyoyi masu zaman kansu, sun kuma nemi a tabbatar da samar da yanayi da muhalli mai tsafta da dalibai za su yi karatu ba tare da barazana ko kuma tsoro ba.

An samar da fiye da Dala Miliyan 30 a lokacin da aka kaddamar da shirin da nufin fitar da tsarin kare makarantu don samar da matasa da zamu iya alfahari da su a jagorancin kasar nan a nan gaba.

Amma kuma wannan mafarki da fata na kungiyar ‘Safe schools’ bai samu cika ba don kuwa an ci gaba da kai hare-hare a makarantu musamman a Arewancin Nijeriya, abin da yake ci gaba da sanya tsoro a kan yiyuwar samar da gyaran da ake bukata a bangaren makarantunmu.

Karuwar hare-haren da kuma garkuwa da ‘yan makaranta da ake ci gaba da yi ya jefa tsoro a zukatan dalibai da iyayensu gaba daya.

Tambaya mai muhimmanci da ya kamata mu yi a wannan lokacin ita ce wai shin menene matsayin kungiyar ‘Safe Schools Initiatibe’ kuma ina fiye da Dala miliyan 30 da aka tara a lokacin kaddamar da kungiyar suka shiga?

Binciken da jaridar nan ta yi kwanakin baya ya nuna cewa, shekaru da dama da kaddamar da shirin ‘Safe Schools Initiatibe’ har zuwa yanzu wasu jihohi da dama basu amfana daga wannan asusun ba, haka kuma basu amfana da shirin kungiyar na kare makarantu ba.

Wannan wani abu ne da ya kamata ya tayar da hankali al’umma da dama musamman ganin kungiyar da ke da alhakin samar da kariya ga makarantumu ta gaza cika alkawarinta. Ana ci gaba da kai hare-hare a makarantunmu babu kakkautawa, a kan haka yana da matukar muhimmanci mu mika ayar tambaya ga masu tafiyar da kungiyar, na su bamu cikakkiyar bayanai na yadda aka sarrafa kudaden da aka tara don al’umma su san yadda aka kashe su.

Barnar da wannan lamari ya yi ga matsalar tsaro yana da matukar girma musamman ganin Nijeriya na da dimbin yara da ke gararamba a kan titi basa zuwa makaranta, an kiyasta cewa, yara fiye da kashi 12.4 na yara wadanda basa zuwa makaranta suna yankin Afrika ta yamnma ne.

Matsalar tsaro ta hana wadanna yara zuwa makaranta, an hana su damar bayar da nasu gudummawarsu ga bunkasar al’ummar yankinsu da kasar su gaba daya.

Ba wai muna jinjina matsalar kawai ba ne, ya kamata mu dauki mataki na kare makarantun don samar wa yaranmu rayuwa nagari.

Muna kira da a gudanar da bincike na musamman a kan yadda aka gudanar da kungiyar ‘Safe Schools’ don gano yadda aka kashe kudaden da aka tara, muna kuma bayar da shawara a tabbatar da wata kungiya ce mai zaman kanta za ta gudanar da binciken don kauce wa zargi da tabbatar da gaskiya.

Dole gwamnati ta muhimmantar da samar da tsaro a makarantumu ta hanyar samar da karin jami’an tsaro a makarantu, a kuma karfafa samar da bayanan sirri da za su kai ga tarwatsa shirin ‘yan ta’adda tare da aikawa da gargadi a duk lokacin da aka samu wasu bayanai da ke nuna akwai wata matsala.

Al’umma na da rawar da za su taka wajen tabbatar da tsaron makarantumu, ya kamata su shiga a dama da su wajen kare makarantunmu ta hanyar bayar da bayanan sirri ga jami’an tsaro da za su kai ga dakile ayyukan ‘yan ta’adda a yankunanmu.

Ya kamata dalibai da malamai da suka fada hannun ‘yan ta’adda su samu tallafi na musamman na kwararru da zai taimaka musu su farfado daga tashin hankalin da suka fuskanta.

Abin takaicin a ra’ayinmu shi ne labarin dalibar makarantar Chibok da aka ceto kwanan nan, inda ta nemi a mayar da ita ga ‘yan ta’addan da suka kama ta. Wannan yana nuna cikakkiyar halin da kasarmu ke ciki ne.

A kan haka muke kira ga gwamnati da masu ruwa da tsaki a harkar ilimi su muhimmantar da lamarin tsaron makarantumu, ta hanyar samar da kudade da kayan aiki ga jami’an tsaro don yin haka tamkar kare kasa ce baki daya. Lokaci ya yi da zamu tabbatar da kare makarantun da kuma kare mutuncinmu.

Kariya
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Next Post
Kwana 100 A Karagar Mulki: Kamun Ludayin Sabbin Gwamnoni

Kwana 100 A Karagar Mulki: Kamun Ludayin Sabbin Gwamnoni

LABARAI MASU NASABA

Falalar Salatut Tasbihi

Falalar Salatut Tasbihi

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.