ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ASUU Ta Yi Kira Ga Majalisar Kasa Ta Cire TETfund Daga Tsarin Sabuwar Dokar Haraji

by Idris Aliyu Daudawa and Sulaiman
2 years ago
Ilimi

Kungiyar Malaman Jami’oi ta kasa ta yi kira da Shugabannin majalisun dattawa da wakilai da cewar su dauki matakan da suka kamata wajen kare hukumar gidauniyar manyan makarantu (TETFund) daga cikin tsarin dokar samar da gyara a al’amuran haraji na shekarar 2024.

A wani jawabin data fitar ranar Jumma’a ta makon daya gabata wadda ke dauke da sa hannun Shugaban kungiyar na kasa,Farfesa Emmanuel Osodeke, ta yi kakkausar sukar cewar dokar idan aka amince da ita a yadda take, zata samar da cikas kan irin muhimmin taimakon da hukumar take badawa ta bangaren ci gaban ilimi.

  • Kudin Kirifto: An Cafke Dan Nijeriya Da Laifin Damfarar ‘Yan Australiya Dala Miliyan 8
  • Bangarorin Da Suka Fi Samun Kaso Mai Tsoka A Kasafin Kudin 2025

“Kungiyar ASUU tana sane da duk halin da ake ciki na maganganun da ake dangane da kawo gyara da samar da doka a tsarin haraji a Nijeriya a shekarar, 2024,wanda a yanzu lamarin yana gaban majalisun kasa.Daga cikin dokar haraji akwai maganar za ayi gyara a dokar harajin daya shafi ilimi kamar yadda lamarin yake,”.

ADVERTISEMENT

Abin da akwai daure kai da ban takaici, domin kuwa sashi na 59 karamin sashi na(3)na dokar ya bayyana cewa kashi 50 na harajin ci gaba za a ba TETFund a shekarun 2025 da 2026 yayin da hukumomin NITDA,NASENL da NELFUND za su raba sauran kashi 50 da ya rage.

Kamar dai yadda lamarin ya ke cewar kungiyar ta ASUU, TETFund, za ta samu kashi “66.7 a shekarar 2027, 2028 da kuma 2029 na shekarun da ake gwada shi lamarin daga nan kuma gaba babu wani abu.

LABARAI MASU NASABA

An Tantance Masu Neman Aikin Koyarwa 500 A Jigawa

JAMB Ta Ƙara Wa’adin Amincewar Guraben Karatu Zuwa 30 Satumba

“ASUU ta damu kwarai dangane da wannan lamari mai hadari na sabuwar dokar haraji,da ake kira harajin ci gaba inda duk wasu tsare- tsaren TETFund za a maida su ga sabuwar hukuma mai suna gidauniyar bada bashin ilimi ta kasa (NELFUND).

“Gaskiyar lamarin shi ne a sanadiyar sabuwar dokar haraji idan har aka amince da ita abin yana nufin daga shekarar 2030, dukkan kudaden da aka samu da suna gidauniyar ci gaba za a rika tura sune zuwa hukumar NELFUND. ASUU tace shi abin ba ma kawai yana da ban takaici bane domin kuwa idan aka kalli ci gaban kasa akwai babbar matsalar da ita hukumar TETFund za ta shiga.

“ASUU ta ci gaba da bayani inda ta ce ba zata kame hannuwanta ba tana ganin ana kokarin kawo karshen ita hukumar TETfund, wadda ita ta kasance ne a matsayin abinda ya biyo bayan zaman da aka yi tsakanin ita kungiyar da gwamnatoci suka yi tun shekarar 1992. A namu ganin idan aka yi gyara a dokar da aka yi a shekarar 2011 ta TETFund, ko dai kawai don ana son ayi hakan ne saboda wani dalili, ba karamin ci baya bane ga lamarin daya shafi ilimi bane kadai, har ma Nijeriya a matsayin ta na kasa.

“Wannan shi yasa domin haka ne, ASUU tana kira majalisun kasa musamman ma Shubannnin majalisun dattawa da ta wakilai ta tarayya, su yi duk iyakar iyarsu su kare TETFund kada ayi amfani da dokar kawo gyara haraji ta 2024,har a kai ga samun damar tarwatsa ta kamar yadda sanarwar ta bayyana.

tetfund
Idris Aliyu Daudawa
+ posts Bio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Rayuwar Galadiman Kano Alhaji Tijjani Hashim (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kyamar Baƙi: An Sake Kwaso Ƴan Nijeriya 83 Daga Afirka Ta Kudu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 60 Da Kayan Aiki A Edo
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tsohon Shugaban Ƙasa Jonathan Ya Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Ƙasa 18 A Jihar Bauchi
tetfund
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

MASU ALAKA

tetfund
Ilimi

An Tantance Masu Neman Aikin Koyarwa 500 A Jigawa

August 31, 2026
tetfund
Ilimi

JAMB Ta Ƙara Wa’adin Amincewar Guraben Karatu Zuwa 30 Satumba

August 29, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Ilimi

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026
Next Post
Mutum 10 Sun Mutu A Turmutsutsin Rabon Shinkafa A Abuja

Mutum 10 Sun Mutu A Turmutsutsin Rabon Shinkafa A Abuja

LABARAI MASU NASABA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.