ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ASUU Ta Yi Kira Ga Majalisar Kasa Ta Cire TETfund Daga Tsarin Sabuwar Dokar Haraji

by Idris Aliyu Daudawa and Sulaiman
2 years ago
Ilimi

Kungiyar Malaman Jami’oi ta kasa ta yi kira da Shugabannin majalisun dattawa da wakilai da cewar su dauki matakan da suka kamata wajen kare hukumar gidauniyar manyan makarantu (TETFund) daga cikin tsarin dokar samar da gyara a al’amuran haraji na shekarar 2024.

A wani jawabin data fitar ranar Jumma’a ta makon daya gabata wadda ke dauke da sa hannun Shugaban kungiyar na kasa,Farfesa Emmanuel Osodeke, ta yi kakkausar sukar cewar dokar idan aka amince da ita a yadda take, zata samar da cikas kan irin muhimmin taimakon da hukumar take badawa ta bangaren ci gaban ilimi.

  • Kudin Kirifto: An Cafke Dan Nijeriya Da Laifin Damfarar ‘Yan Australiya Dala Miliyan 8
  • Bangarorin Da Suka Fi Samun Kaso Mai Tsoka A Kasafin Kudin 2025

“Kungiyar ASUU tana sane da duk halin da ake ciki na maganganun da ake dangane da kawo gyara da samar da doka a tsarin haraji a Nijeriya a shekarar, 2024,wanda a yanzu lamarin yana gaban majalisun kasa.Daga cikin dokar haraji akwai maganar za ayi gyara a dokar harajin daya shafi ilimi kamar yadda lamarin yake,”.

ADVERTISEMENT

Abin da akwai daure kai da ban takaici, domin kuwa sashi na 59 karamin sashi na(3)na dokar ya bayyana cewa kashi 50 na harajin ci gaba za a ba TETFund a shekarun 2025 da 2026 yayin da hukumomin NITDA,NASENL da NELFUND za su raba sauran kashi 50 da ya rage.

Kamar dai yadda lamarin ya ke cewar kungiyar ta ASUU, TETFund, za ta samu kashi “66.7 a shekarar 2027, 2028 da kuma 2029 na shekarun da ake gwada shi lamarin daga nan kuma gaba babu wani abu.

LABARAI MASU NASABA

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

“ASUU ta damu kwarai dangane da wannan lamari mai hadari na sabuwar dokar haraji,da ake kira harajin ci gaba inda duk wasu tsare- tsaren TETFund za a maida su ga sabuwar hukuma mai suna gidauniyar bada bashin ilimi ta kasa (NELFUND).

“Gaskiyar lamarin shi ne a sanadiyar sabuwar dokar haraji idan har aka amince da ita abin yana nufin daga shekarar 2030, dukkan kudaden da aka samu da suna gidauniyar ci gaba za a rika tura sune zuwa hukumar NELFUND. ASUU tace shi abin ba ma kawai yana da ban takaici bane domin kuwa idan aka kalli ci gaban kasa akwai babbar matsalar da ita hukumar TETFund za ta shiga.

“ASUU ta ci gaba da bayani inda ta ce ba zata kame hannuwanta ba tana ganin ana kokarin kawo karshen ita hukumar TETfund, wadda ita ta kasance ne a matsayin abinda ya biyo bayan zaman da aka yi tsakanin ita kungiyar da gwamnatoci suka yi tun shekarar 1992. A namu ganin idan aka yi gyara a dokar da aka yi a shekarar 2011 ta TETFund, ko dai kawai don ana son ayi hakan ne saboda wani dalili, ba karamin ci baya bane ga lamarin daya shafi ilimi bane kadai, har ma Nijeriya a matsayin ta na kasa.

“Wannan shi yasa domin haka ne, ASUU tana kira majalisun kasa musamman ma Shubannnin majalisun dattawa da ta wakilai ta tarayya, su yi duk iyakar iyarsu su kare TETFund kada ayi amfani da dokar kawo gyara haraji ta 2024,har a kai ga samun damar tarwatsa ta kamar yadda sanarwar ta bayyana.

tetfund
Idris Aliyu Daudawa
+ posts Bio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
tetfund
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
  • Sulaiman
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
  • Sulaiman
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

MASU ALAKA

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
Ilimi

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
Ilimi

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Next Post
Mutum 10 Sun Mutu A Turmutsutsin Rabon Shinkafa A Abuja

Mutum 10 Sun Mutu A Turmutsutsin Rabon Shinkafa A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.