ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Atiku Ya Bukaci Majalisar Dattawa Ta Gaggauta Gyara Dokar Zabe Don Hana Magudi A 2027

by Yusuf Shuaibu
5 months ago
Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya bukaci majalisar dattawan Nijeriya da ta yi hanzarin sake dubawa da amincewa da gyara dokar zabe ta 2022, yana gargadin cewa gibin da ke cikin doka ya taimaka wajen samun rashin daidaito a lokacin zaben 2023.

A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Atiku ya bayyana cewa tsarin doka na yanzu ya sa ya zama ba zai yiwuwa ba ga masu daukar karar su gabatar da shari’o’insu a kotu,” wanda ya haifar da yanayi da ya bai wa abin da ya bayyana a matsayin babban magudi a shekarar 2023.

  • An Nada Liu Xianfa Wakilin Musamman Na Gwamnatin Sin Kan Harkokin Afirka
  • CGI Babandede Mai Ritaya A Mizanin Kyawawan Halaye Da Kwazon Aiki

Ya jaddada cewa gyara wadannan kurakurai yana da muhimmanci don gudanar da sahihin zabe a 2027, yana karfafa ‘yan majalisa su tabbatar sun amince da kowace gyara a kan lokaci don jagorantar zabe na gaba.

ADVERTISEMENT

“A lokacin da kurakuran zabukan shekarar 2023 kenan a fili, wajibi ne a sake duba dokokin da ake amfani da su wajen gudanar da zabukan 2027 da na gaba,” in ji Atiku.

Ya nuna damuwa kan yadda majalisar dattawa ta kuduri aniyar jinkirta ko kawo cikas ga zartar da gyare-gyare, yana mai ambaton rahoton kwanan nan da Gidauniyar Aikin Jarida ta Bincike (FIJ) ta yi a matsayin tuhuma na rashin daukar mataki na majalisa.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

“Sahihin zabe a 2027 ya dogara ne kan gaggawar da majalisar dattawa za ta nuna wajen daukar mataki kan wannan muhimmin doka. Yana da matukar muhimmanci ga majalisar dattawa ta kammala gyare-gyaren dokar kuma ta tabbatar cewa sabon doka ce ke tsara yadda za a gudanar da zaben 2027. Rashin yi hakan, nana cewa akwai yunkurin yin magudi a jefa kuri’u,” in ji Atiku.

“Babbar koma baya ga zaben 2023 ita ce, wagegen gibin da ke cikin dokar zabe ta 2022, wanda ya ba da damar yin magudi a bude a wannan zaben, da kuma rashin bai wa masu koke damar gabatar da shari’arsu a gaban kotu.

“Yana da muhimmanci idan za a gyara kurakuran zaben shekarar 2023, ya kamata a sake duba dokokin don toshe hanyoyin magudi a zaben 2027 da mana gaba.

“Amma a halin da ake ciki, a bayyane yake cewa majalisar dattawa ta kuduri aniyar kawo cikas ga gyare-gyaren dokar zabe ta 2022.

“Rahoton da gidauniyar FIJ ta fitar kwanan nan yana matsayin zargin majalisar dattawa da kuma kiran gaggawa na sauke alhakin dokoki. Gudanar da sahihin zabe a 2027 yana dogara ne kan gaggawar da majalisar dattawa za ta nuna wajen magance wannan muhimmin kudiri.

“Saboda haka, yana da muhimmanci majalisar dattawa ta kammala sauye-sauyen dokokin kuma ta tabbatar da cewa dokar ta zamani ce ke za ta kula da gudanar da zaben shekarar 2027. Kasa da wannan kokari na nufin tsara zabe tun kafin a jefa kuri’u.”

Atiku
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
2027: Watsi Da Muslim-muslim Tiket Zai Iya Raunata APC — Ministar Al’adu

2027: Watsi Da Muslim-muslim Tiket Zai Iya Raunata APC — Ministar Al’adu

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.