ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Atiku Ya Bukaci Majalisar Dattawa Ta Gaggauta Gyara Dokar Zabe Don Hana Magudi A 2027

by Yusuf Shuaibu
4 months ago
Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya bukaci majalisar dattawan Nijeriya da ta yi hanzarin sake dubawa da amincewa da gyara dokar zabe ta 2022, yana gargadin cewa gibin da ke cikin doka ya taimaka wajen samun rashin daidaito a lokacin zaben 2023.

A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Atiku ya bayyana cewa tsarin doka na yanzu ya sa ya zama ba zai yiwuwa ba ga masu daukar karar su gabatar da shari’o’insu a kotu,” wanda ya haifar da yanayi da ya bai wa abin da ya bayyana a matsayin babban magudi a shekarar 2023.

  • An Nada Liu Xianfa Wakilin Musamman Na Gwamnatin Sin Kan Harkokin Afirka
  • CGI Babandede Mai Ritaya A Mizanin Kyawawan Halaye Da Kwazon Aiki

Ya jaddada cewa gyara wadannan kurakurai yana da muhimmanci don gudanar da sahihin zabe a 2027, yana karfafa ‘yan majalisa su tabbatar sun amince da kowace gyara a kan lokaci don jagorantar zabe na gaba.

ADVERTISEMENT

“A lokacin da kurakuran zabukan shekarar 2023 kenan a fili, wajibi ne a sake duba dokokin da ake amfani da su wajen gudanar da zabukan 2027 da na gaba,” in ji Atiku.

Ya nuna damuwa kan yadda majalisar dattawa ta kuduri aniyar jinkirta ko kawo cikas ga zartar da gyare-gyare, yana mai ambaton rahoton kwanan nan da Gidauniyar Aikin Jarida ta Bincike (FIJ) ta yi a matsayin tuhuma na rashin daukar mataki na majalisa.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

“Sahihin zabe a 2027 ya dogara ne kan gaggawar da majalisar dattawa za ta nuna wajen daukar mataki kan wannan muhimmin doka. Yana da matukar muhimmanci ga majalisar dattawa ta kammala gyare-gyaren dokar kuma ta tabbatar cewa sabon doka ce ke tsara yadda za a gudanar da zaben 2027. Rashin yi hakan, nana cewa akwai yunkurin yin magudi a jefa kuri’u,” in ji Atiku.

“Babbar koma baya ga zaben 2023 ita ce, wagegen gibin da ke cikin dokar zabe ta 2022, wanda ya ba da damar yin magudi a bude a wannan zaben, da kuma rashin bai wa masu koke damar gabatar da shari’arsu a gaban kotu.

“Yana da muhimmanci idan za a gyara kurakuran zaben shekarar 2023, ya kamata a sake duba dokokin don toshe hanyoyin magudi a zaben 2027 da mana gaba.

“Amma a halin da ake ciki, a bayyane yake cewa majalisar dattawa ta kuduri aniyar kawo cikas ga gyare-gyaren dokar zabe ta 2022.

“Rahoton da gidauniyar FIJ ta fitar kwanan nan yana matsayin zargin majalisar dattawa da kuma kiran gaggawa na sauke alhakin dokoki. Gudanar da sahihin zabe a 2027 yana dogara ne kan gaggawar da majalisar dattawa za ta nuna wajen magance wannan muhimmin kudiri.

“Saboda haka, yana da muhimmanci majalisar dattawa ta kammala sauye-sauyen dokokin kuma ta tabbatar da cewa dokar ta zamani ce ke za ta kula da gudanar da zaben shekarar 2027. Kasa da wannan kokari na nufin tsara zabe tun kafin a jefa kuri’u.”

Atiku
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
2027: Watsi Da Muslim-muslim Tiket Zai Iya Raunata APC — Ministar Al’adu

2027: Watsi Da Muslim-muslim Tiket Zai Iya Raunata APC — Ministar Al’adu

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.