Masu Binciken Sin Sun Kammala Gwajin Sadarwa Tsakanin Duniyar Dan Adam Da Ta Wata Ta Amfani Da Fasahar Laser
Masu bincike na kasar Sin sun kammala gwajin sadarwa tsakanin duniyar dan Adam da duniyar wata, inda suka yi nasarar...
Masu bincike na kasar Sin sun kammala gwajin sadarwa tsakanin duniyar dan Adam da duniyar wata, inda suka yi nasarar...
Daga ranar 31 ga watan Agustan da muke ciki zuwa ranar 1 ga watan Satumba mai zuwa, za a gudanar...
Kasar Sin ta mika aikin gyara da fadada asibitin Masaka na Rwanda ga hukumomin kasar, yayin wani biki da ya gudana jiya Juma’a a babban birnin Kigali. Aikin wanda Sin ta bayar da tallafin gudanar da shi, shi ne aikin tallafi mafi girma da gwamnatin Sin ta gudanar a Rwanda, kuma wani muhimmin aiki na inganta rayuwa da ke karkashin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya. Biyo bayan gyara da fadada asibitin, girmansa ya karu daga murabba’in mita 6,398 zuwa murabba’in mita 56,957, yayin da adadin gadaje ya karu sosai daga 127 zuwa 837. An kuma samu karuwar adadin marasa lafiya da asibitin zai iya karba a kullum zuwa 2,000. Da yake jawabi yayin bikin, ministan lafiya na kasar Sabin Nsanzimana, ya ce wannan wani gagagrumin ci gaba ne ga kasar da kuma bangaren kiwon lafiya. Ya ce suna sa ran wannan asibiti zai zama alama ta ingantacciyar kiwon lafiya da za su iya samarwa a Rwanda da nahiyar Afrika. Kuma suna sa ran ci gaba da hada hannu da Sin don ganin hadin gwiwar ta fadada a bangaren kiwon lafiya. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)
Kafin ziyarar aiki a Masar da shugaban Sin Xi Jinping zai yi, babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin...
An Kai Kayayyakin Agaji Masu Yawa Zuwa Gyirong Na Yankin Hukumar kai dauki da ba da agajin gaggawa ta yankin Xizang ta bayyana a jiya Alhamis cewa, an kai kayayyakin agaji masu yawa zuwa garin Gyirong na birnin Xigaze, ciki har da shinkafa tan 50 da garin alkama tan 20 da man girki tan 1, da kuma tantuna 1,122, da barguna 8,054, kana da injunan samar da wutar lantarki 14, da fakitin ruwan sha 15,500, da sauran kayayyakin amfanin yau da kullum. Bayan haka, an tura kwararru 86 daga fannoni daban-daban kamar albarkatun kasa zuwa yankin da ibtila'in ya shafa, tare da kayan aiki na musamman, don karfafa bincike kan hadurran yanayin kasa a kewayen yankin, da kuma duba manyan wuraren dake da hatsarin abkuwar ibtila'i kamar tsaunuka da hanyoyi da gine-gine da sauransu, don rigakafin sake abkuwar wani ibtila’i ko kuma ibtila’i mai biyo baya. Ya zuwa yanzu, an kammala tsugunar da mutane 499 da ibtila'in zabtarewar kasa da laka ya shafa, kuma an kwashe masu yawon bude ido 555 da suka makale. Kazalika, hukumar ta kara da cewa, wannan ibtila'in zabtarewar kasa da laka a Gyirong na yankin Xizang, lamari ne mai sarkakiya wanda ya samo asali daga zabtarewar kankara mai tsayi a kasar Nepal, inda ya haifar da kwararar tarkacen kankara, sannan ya canja zuwa zabtarewar kasa da laka. (Amina Xu)
Da safiyar yau Jumma'a, ofishin yada labarai na majalisar gudanarwa ta Sin ya gudanar da taron manema labarai, inda ya...
A yau Jumma’a, ma’aikatar kula da masana’antu da fasahar sadarwa ta kasar Sin ta sanar da cewa, tun daga farkon...
A yau Jumma’a, Xi Jinping, babban sakataren kwamitin tsakiya na Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin (JKS), ya jagoranci taron shugabanni na jam’iyyar domin tattaunawa da fitar da tsare-tsaren ayyukan ceto da ba da agaji, bayan abkuwar mummunar zabtarewar kasa a gundumar Gyirong, da ke jihar Xizang mai cin gashin kanta, a kudu maso yammacin kasar Sin. A farkon taron dai, Xi wanda har ila yau shi ne shugaban kasar Sin kuma shugaban hukumar soja ta tsakiya, tare da sauran shugabanni, sun yi shiru na dan lokaci domin nuna alhini game da wadanda ibtila’in ya shafa, wanda ya abku a gundumar Gyirong da ke kan iyakar Nepal da Sin, a ranar Larabar da ta gabata. Taron ya yi nuni da cewa, ibtila’in malalar baraguzai daga bangaren kasar Nepal, ya haifar da asarar rayuka da dama tare da katse hanyoyin sadarwa a kan iyaka ta Gyirong da ke gundumar Gyirong, a birnin Xigaze na jihar Xizang. Bayan abkuwar lamarin, kwamitin tsakiya na JKS ya ba shi muhimmanci sosai, inda babban sakatare Xi Jinping ya bayar da muhimman umarni nan take, tare da gabatar da abubuwan da ake bukata takamaime game da ayyukan ceto da daukar matakan gaggawa na ba da agaji. Bisa sahalewar babban sakataren, firaminista Li Qiang ya garzaya zuwa wurin da ibtila’in ya abku domin ziyara da kuma rarrashin wadanda lamarin ya shafa da karfafa gwiwar ma’aikatan ceto, tare da bayar da jagoranci kai-tsaye a wurin kan ayyukan ceto da daukar matakan gaggawa na ba da agaji. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
'Yan siyasar kasashen yamma kan karawa batun "rarar kayan da Sin ta samar" gishiri, amma a Afirka, an kira shi...
Masana’antar sarrafa bayanai ta kasar Sin ta ci gaba da fadada cikin sauri a shekarar 2025, inda take tallafa wa...
© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.
© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.