Batun Kammala Aikin Gina Gidaje 250 Na “Renewed Hope” Ya Bar Baya Da Kura A Jihar Katsina
Ministan gidaje da raya birane, Muttaqa Rabe Darma, ya bayyana rashin gamsuwarsa da yadda aikin gina gidaje 250 ƙarƙashin shirin “Renewed Hope” na gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ke gudana a Jihar Katsina.
Ministan ya bayyana hakan ne yayin wata ziyarar gani da ido domin duba yadda aikin ke gudana a rukunin gidajen da ke kusa da Jami’ar Umaru Musa Yar’Adua da ke Jihar Katsina.
Injiniya Muttaƙa Rabe Darma ya ce rahoton da ya karanta a ofis ya nuna cewa an kammala gina gidaje 250 ɗin gaba ɗaya, saɓanin abin da ya gani da idonsa yayin ziyarar.
Ya ce: “An rubuta a rahoto cewa gidaje 250 ƙarƙashin shirin shugaban ƙasa na ‘Renewed Hope’ an kammala su gaba ɗaya a Katsina, amma da na zo nan, guda 130 ne kawai aka kammala, kamar yadda kowa ya gani.”
A cewarsa, ya bayar da umarnin a nemo ‘yan kwangilar domin jin dalilan da suka sa ba su kammala aikin ba kamar yadda aka ƙulla yarjejeniya da su tun farko.
Ministan ya yi barazanar ɗaukar mataki a kan duk wani ɗan kwangilar da aka samu da karya alƙawari ba tare da wani kwakkwaran dalili ba.
Ya ƙara da cewa, yarjejeniyar da aka ƙulla da ‘yan kwangilar ita ce, su kammala aikin cikin watanni shida, amma yanzu kusan shekara ɗaya da rabi kenan tun bayan bayar da aikin ba tare da an kammala shi ba.
Haka kuma, ya ce babu wani bayani a rubuce daga wajen ‘yan kwangilar dangane da jinkirin aikin.
Ministan ya bayyana cewa babu inda aka ambaci ƙarin wa’adin kwangila a cikin yarjejeniyar da aka sanya hannu tsakanin gwamnati da ‘yan kwangilar kafin a ba su aikin.
Ya ce: “Babu wani dalili da ‘yan kwangila za su bayar da zai gamsar da gwamnati kan rashin kammala aikin cikin wa’adin da aka tsara.”
Dangane da matakin da gwamnati za ta ɗauka, ministan ya ce hakan zai shafi ne kawai waɗanda ba su kammala ayyukansu ba, yayin da waɗanda suka cika sharuddan kwangila ba za a ɗauki wani mataki a kansu ba.















Discussion about this post