Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yanke wa wani da rikicin Boko Haram ya rutsa da shi, Ali Kolo, hukuncin ɗaurin shekaru tara a gidan yari, duk da cewa ya shafe sama da shekaru 10 a tsare yana jiran shari’a.
Mai shari’a, Justice Peter Odo Lifu, ya kuma bayar da umarnin a sake shi nan take, yana mai cewa wanda aka yankewa hukuncin ya riga ya shafe fiye da wa’adin da kotu ta yanke masa.
- Kotu Ta Dakatar da Taron ADC A Adamawa Saboda Rikicin Cikin Gida
- Kotu Ta Ɗage Sauraron Neman Beli Na El-Rufai Zuwa Gobe Laraba
Kotun ta same shi da laifin rashin sanar da hukumomin tsaro bayanai kan ayyukan ƙungiyar Boko Haram, duk da cewa ya samu raunin harbin bindiga a kafarsa daga ‘yan ƙungiyar a Jihar Borno yayin da yake ƙoƙarin kai rahoto ga sojoji.
Lauyan gwamnati, David Kaswe, ya ce wanda ake tuhuma ya kasa sanar da jami’an tsaro bayanai a shekarar 2017 kamar yadda doka ta tanada, yayin da lauyarsa, A.O. Usman, ta roƙi sassauci tana mai cewa an harbe shi ne yayin da yake kan hanyar kai rahoton, lamarin da ya hana shi isa wurin jami’an tsaro.
A hukuncin da ya yanke, mai shari’ar ya ce duk da laifin da aka same shi da shi, yanayin da ya shiga ne ya hana shi cika wannan wajibcin. Don haka ya umarci a fara kirga hukuncin tun daga shekarar 2017, yana mai jaddada cewa ci gaba da tsare shi zai zama kamar hukunta shi sau biyu, tare da ba da umarnin a sake shi domin kula da lafiyarsa.















Discussion about this post