Shugaban jam’iyyar ADC na Ƙaramar Hukumar Tambuwal a jihar Sakkwato, Bello Ibrahim Tambuwal (Dan- Marafa) ya bayyana cewar duk wani bincike da Hukumar EFCC za ta yi wa Atiku Abubakar bi- ta da ƙullin siyasa ne saboda gwamnatin APC ta hango faɗuwa a zaɓen da ke tafe.
Ya ce gagarumar karɓuwar Atiku a wajen ‘yan Nijeriya da matsayarsa kan dawo da tallafin mai, da sake buɗe boda, da tallafin aikin Hajji da magance matsalar tsaro sun tsorata tare da rikita gwamnatin Tinubu.
Ya ce bayan Atiku ya kwashe shekaru 19 da sauka a matsayin Mataimakin Shugaban Ƙasa dukka hukumomin EFCC da ICPC ba su tashi binciken sa ba sai yanzu da ake daf da zaɓe wanda hakan ya nuna jam’iyya mai mulki na ƙoƙarin razana ‘yan adawa ne tare da kare lagonsu kuma ba za su yi tasiri ba.
A cewarsa duk wani ƙoƙarin da jam’iyya mai mulki ko wasu ƙungiyoyi ke yi kan wannan binciken kuskure ne domin farin jini da ƙarin karɓuwa suka jawowa Atiku a yayin da jama’a ke ƙara dawowa daga rakiyar mulkin APC.














