• Leadership Hausa
Sunday, June 4, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Sake Fasalin Yadda Ake Karbar Sabon Katin Zabe

by Bello Hamza
5 months ago
in Bakon Marubuci
0
Bukatar Sake Fasalin Yadda Ake Karbar Sabon Katin Zabe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tuni dai aka fara karbar katin zabe na dindin a dukkan kananan hukumomin kara nan kamar yadda Hukumar Zabe mai Zaman Kanta (INEC) ta sanar, ta ce, za a fara karbar sabon katin ne a tsakanin ranakun 12 ga watan Disamba zuwa ranar 22 ga watan Janairu na shekarar 2023.

Hukumar ta zartar da cewa, za a cigaba da karbar katin ne a cibiyoyin rajista a mazabu 8,809 na fadin tarayyar kasar nan a tsakanin ranakun da aka zayyana na ranakun 6 zuwa 15 ga watan Janairu shekarar 2023.

  • Hada Rubutu Da Karantarwa Ne Babban Kalubalen Da Nake Fuskanta -Amira Sule
  • Gwamnatin Kano Ta Tunbuke Kwamishinan Addinai Kan Rashin Mata Biyayya

Rahottanin da suke fitowa daga cibiyoyin kabar ya nuna cewa, Shirin karbar katin yana gamuwa da cikas na abin da ya shafi cunkoso da rudanin rashin tantanace masu karbar katin.

Haka kuma karbar katin a yankin babban birnin tarayyar kasar nan Abuja ya nuna cewa, an karbar katin a lokaci daya a dukkan kananan hukumomi 6 na birnin tarayyar.

A wasu cibiyoyin karbar katin a yankin Abuja, al’umma da suka yi rajista na taruruwan sun sun fito domin karbar katin amma babu isassun ma’aikatan da za su saurare su tare da basu katin zaben, cunkoson ya haifar da babbar matsala a wasu cibiyon kabar katin.

Labarai Masu Nasaba

Wutar Bashi: Tukunyar Bashin Wasu Jihohi 8 Na Kan Zabalbala

Ninkayar Kano A Kogin Basukan Gida Da Daji

Haka kuma an samu bayanan cewa, an cigaba da bayar da katin a wasu mazabu, duk da cewa hakan ya danganta ne da yadda mutum ya yi rajistar tunda farko yin rajistar, ko mutum ya tashi ne daga wani gari zuwa wani ko kumu yana neman a sake masa katin a dalilin bacewa ko salwanta, ko kuma wasu dalilai na daban.

Kamar yadda aka yi tunani al’umma da dama da suka tattauna da manema labari sun nuna damuwarsu a kan yadda shirin rarraba katin ke gudana, wasu na yabawa wasu kuma na nuna damuwarsu a kan yadda ake bayar da katin. A yayin da wasu da aka tattauana da su suka jinjina tare da yabawa da yadda jami’an hukumar INEC suke tafiyar da shirin raba katin sai dai sun yi korafin yadda ba a yi cikakken tsarin ba, abin da ya kai ga wahalar da mutane da dama da suka nufi cibiyoyin karbar katin zabensu na dindindin.

A mastayinmu na dan jarida mun yi imanin cewa, bai kamata a ce, karbar katin zaben ya zama wani abin da za a sha wahala a kai ba. Tunda akwai sauran lokaci da aka ayyana na karbar katin ya kamata a ce, INEC ta kara kaimin yadda take gudanar da shirin.

Muna sane da yadda hukumar ke fama matsalolin gurbatattun ‘yan siyasa da ke kokarin kawo cikas ga tsarin shirin gudanar da zaben gaba daya don cimma burin kashin kansu. Tabbas ina sane cewa, INEC na fuskantar manyan matsaloli a halin yanzu.

Amma kuma in aka lura da yadda aka fuskanci rudai a lokacin da aka yi rajistar yakamata a ace an dauki darussa ta yadda karbar katin a wanna lokacin ya zama a cikin sauki ga masu karbar katin a sassan Nijeriya. Tun da aka fara fuskantar wadannan matsalolin yakamata a ce, INEC ta dauiki matakin sake fasalin yadda ake rarraba katin duk shi dan Nijeriya gwamnace ya yi komai a lokacin da al’amurra suka kure.

Ana iya ganin wannan a lokacin da aka yi rajistar katin inda sai daga karshe mutane suka yi ta tururwa don katin abin da sanya har sai da aka ta kiraye-kirayen neman a kara wa’adin cigaba da bayar da katin, magana har sai da ta kai ga hukuncin kotu na nemi a kara wa’adin lokacin yin rajistar.

A kan haka yakamata ace. Hukumar ta samar ya yanayin da karbar ya zo a cikin sai tun a karon farko don a kulle bakin masu kokarfi wadanda basu ganin alhairi a dukkan ayyukan da hukumar take yi a dukkan lokaci.

Kamar dai yadda ta yi a lokacin da ake yi wa al’umma rajistar kantin zaben, yakamata a INEC ta samar da cibiyoyin karbar katin zabe a kusa da al’umma tare da kuma fadakar da mutane bukatar fitowarsu don karbar katin zaben domin kuwa in har mutum bashi da katin zaben bashi ba zabe a 2023.

Dokar zabe ta shekara 2023 ta tanadi cewa, dole sai in mutum yana da katin zabe ne akwai zai samu damar kada kuri’a a kan dole ta samar da yanayin da kowa zai samu karbar katin zaben don ya sauke nauyin da ke kansa na zaban wanda yake so ya mulke shi a shekarar 2023.

Ya kuma kamata jam’iyyun siyasa su kara kaimi wajen fadakar da mambobin su a kan bukatar fitowa don su karbi katin zaben ba wai kawai su bar wa gwamnati aikin fadakawar ba. A daidai lokacin da muke da kasa da kwanaki 50 zuwa ranar da za a gudanar da zaben, lallai babu wani lokaci da za a bata.

Tags: INECKatin Zabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ko Kun San Irin Bakar Wuyar Da Ake Sha Wajen Tantance Gawarwaki A Yakin Ukraine?

Next Post

Mutanen Arewa Ba Su Da Wata Hujjar Kin Zabar Tinubu — Ganduje

Related

Wutar Bashi: Tukunyar Bashin Wasu Jihohi 8 Na Kan Zabalbala
Bakon Marubuci

Wutar Bashi: Tukunyar Bashin Wasu Jihohi 8 Na Kan Zabalbala

1 week ago
Ninkayar Kano A Kogin Basukan Gida Da Daji
Bakon Marubuci

Ninkayar Kano A Kogin Basukan Gida Da Daji

2 weeks ago
Tozon Basuka A Jihohin Kano Da Kaduna
Bakon Marubuci

Tozon Basuka A Jihohin Kano Da Kaduna

3 weeks ago
Zabe
Bakon Marubuci

Mirginawar Rumbun Basuka A Jihohin Kano Da Kaduna

4 weeks ago
Nijeriya
Bakon Marubuci

Kididdigar Basukan Gwamnatoci A Jamhuriya Ta Hudu

1 month ago
Baba Buhari: Madugun Cin Bashi A Jamhuriya Ta Hudu
Bakon Marubuci

Baba Buhari: Madugun Cin Bashi A Jamhuriya Ta Hudu

1 month ago
Next Post
Tinubu Ya Amince Zai Dauki Musulmi A Matsayin Mataimakinsa —Ganduje

Mutanen Arewa Ba Su Da Wata Hujjar Kin Zabar Tinubu — Ganduje

LABARAI MASU NASABA

Hajjin Bana: Adadin Alhazan Nijeriya A Saudiyya A Yanzun Ya kai 24,324 

Hajjin Bana: Adadin Alhazan Nijeriya A Saudiyya A Yanzun Ya kai 24,324 

June 4, 2023
Tawagar Sojin Injiniya Ta Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Kasar Sin Ta Tallafawa Kongo Kinshasa Ta Fuskar Aikin Ceto

Tawagar Sojin Injiniya Ta Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Kasar Sin Ta Tallafawa Kongo Kinshasa Ta Fuskar Aikin Ceto

June 4, 2023
Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

Gwamna Yusuf Ya Kori Jami’an Cibiyar Alhazan Kananan Hukumomi 44 Na Jihar Kano

June 4, 2023
Me Ya Sa BRICS Ke Kara Samun Karbuwa Daga Kasashen Duniya

Me Ya Sa BRICS Ke Kara Samun Karbuwa Daga Kasashen Duniya

June 4, 2023
Sana’ar Kwalliya

Sana’ar Kwalliya

June 4, 2023
Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli

Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli

June 4, 2023
Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

June 4, 2023
Takaitaccen Tarihin Ka’idojin Rubutun Hausa (II)

Takaitaccen Tarihin Ka’idojin Rubutun Hausa (II)

June 4, 2023
Dalilin Da Manoman Rama A Jihar Katsina Ke Kara Habaka

Dalilin Da Manoman Rama A Jihar Katsina Ke Kara Habaka

June 4, 2023
Farashin Tumatir Ya Karye Bayan Ghana Da Kamaru Sun Turo Shi Kasuwannin Nijeriya

Farashin Tumatir Ya Karye Bayan Ghana Da Kamaru Sun Turo Shi Kasuwannin Nijeriya

June 4, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.