Sin ta fara aiwatar da manufar soke harajin fito gaba daya ga kasashe 53 na Afirka da suka kulla dangantakar diplomasiyya da ita daga ran 1 ga watan Mayun bana. Bayan watanni uku da rabi, Najeriya ta amfana sosai da wannan manufa. A kwanan nan kafafen yada labarai na kasar na cewa, a rabin farkon bana, yawan kayayyaki da Najeriya ta fitar da su zuwa kwasuwannin kasar Sin ya karu da kashi 80%, inda darajarsu ta kai dala biliyan 2.3, kuma an samu karuwar da ta wuce kashi 40% a watannin Mayu da Yuni. Gwamnatin tarayyar Najeriya ta yi amfani da wannan dama don inganta kwaskwarima ta hanyar karkata tsarinta na fitar da kayayyaki, wato daga fitar da danyen kayayyaki ko kayayyakin da aka dan sarrafa zuwa fitar da kayayyakin noma da kayayyakin ma’adanai masu karin daraja, da kayayyakin masana’antu da aka sarrafa su sosai.Batun nan ya bayyana yadda aka hada tsarin bude kofa bisa manufofin ketare da Sin ke dauka da bukatun neman ci gaba na kasashen Afirka tare.
Ministan ma’aikatar noma da samar da isasshen abinci na Najeriya Aliyu Sabi Abdullahi, a wani taron karawa juna sani kan “Manufar soke haraji ta Sin da sauyin tsarin tattalin arzikin Afirka”, wanda aka gudanar kwanan nan a Najeriya, ya ce “Manufar soke haraji kadai ba za ta tabbatar da samun ci gaban da muke bukata ba”. Kalaman ministan sun bayyana abin da Najeriya ke karin bukata bisa matakin da Sin ke dauka, watau baya ga manufar soke haraji, Sin na samar da damarmakin da ke taimaka wa Najeriya wajen inganta karfinta na cin moriya tare.
Yayin taron, jakadan Sin a Najeriya Yu Dunhai ya bayyana cewa, bangaren Sin yana son ba da tallafin fasaha a fannin samar da kayayyaki, don kara ingancin kayayyakin Najeriya da samun damar fadada shiga kasuwar Sin. Wannan shi ne mabudin fadada hadin gwiwar Sin da Afirka daga “mu’ammalar ciniki” zuwa “bunkasa karfi tare da cin moriya tare”.
Alal hakika, fa’idojin hadin gwiwar cinikayya tsakanin Sin da Najeriya sun riga sun bayyana sakamako na a zo a gani. Jakada Yu ya ce, masu fitar da kayayyaki na Najeriya za su iya yin tsimin kudin haraji kusan dala dubu 11 a kowane ton 100 na ridin da za su fitarwa Sin, kana za a yi tsimin kudin haraji kusan dala dubu 450 idan aka fitarwa Sin gutsurarrun kashin saniya tan dubu 7 a kowace shekara. Ban da wannan kuma, a ranar farko da aka fara aiwatar da manufar, ’yan kasuwar Najeirya sun yi tsimin kusan dala dubu 300 wajen fitar wa Sin iskar Propane mai ruwa tan dubu 23.
Wadannan alkaluma suna nufin cewa, kudin shigar manoman Najeriya ya karu, kwarin gwiwar masana’antar sarrafa kayayyaki ya karu, kuma guraben ayyukan yi sun karu.Canji mafi zurfi ya zo a bangaren yi wa tsarin cinikayya kwaskwarima a Najeriya. Da ma Najeriya tana fitar da kayayyakin noma da ba a sarrafa su ba da danyen ma’adanai zuwa Sin, amma bayan Sin ta aiwatar da wannan manufa, ta bai wa Najeriya damammakin fitar da kayayyakin noma na musamman da kayan ma’adanai masu karin daraja da aka sarrafa, zuwa kasuwar Sin cikin sauri.
Hadin gwiwar Sin da Najeriya ba wai kawai “hadin kai ne a kan ababen more rayuwa” ba, har ma da “zurfafa hadin gwiwa a bangaren masana’antu da kasuwa”, bayan rabin karni da kafuwar dangantakarsu ta diplomasiyya. Kuma Sin ba samar wa Najeriya damar shiga kasuwa kadai ta yi ba, har ma da taimaka mata wajen kafa cikakken tsari kan kowane nau’in kaya da za ta fitar zuwa Sin, bisa tallafin kimiyya da fasaha da hadin gwiwar masana’antu, ta yadda Najeriya za ta daina fitar da danyen ma’adinai da kayayyakin da ba a sarrafa ba, matakin da ya bayyana sabon nau’in hadin gwiwar Sin da Afirka wanda ya zama abin koyi, wato hadin gwiwa da cin moriya tare.(Marubuciya:MINA)













