ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya

by Abubakar Abba
3 weeks ago
Kiwo

Gwamnatin tarayya, ta danganta rashin samun sahihan bayanai a matsayin babban ginshikin da ke sanya wa ana ci gaba da samun gibi a fannin kiwon dabbobin kasar.

Ta kara da cewa, matsalar ta fi yin kamari, a bangaren yin reno da kuma tattalin dabbobin, domin kara samar da wadatunsu a fadin kasar baki-daya.

Ministan Ma’aikar Kula da Bunkasa Kiwon Dabbobi, Idi Mukhtar Maiha, ya yi gargadin cewa; matukar ba a samu cikakkun sahihan bayanai kan renon dabbobin kasar ba, hakan zai yi matukar wuya wajen bunkasawa da kuma ci gaba da samar da jinsin dabbobin a Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Maiha, ya yi wannan gargadin ne a taron bita, domin tattaunawa da masu ruwa da tsaki a Abuja.

Sashen samar da jinsin dabbobi da ke ma’aikata ne ya shirya taron, a karkashin aikin habaka dabbobi da kuma bayar da dauki wato, lPRSP.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Manoma 2,930 Buhun Taki 11,720 A Abuja

Ku Gaggauta Fara Yin Shuka A Kakar Bana: Saƙon Hukumar NiMet Ga Manoma

“Idan har ba a samar da sahihan bayanan a fannin na kiwon kasar ba, zai yi wuya a iya cimma burin da ake da shi, wajen gano irin nau’in dabbobin da suka dace a yi renonsu, musamman nau’in irin wadanda za su kasance da kowane irin yanayi na shiyyar kasar,” a cewarsa.

Kazaika, mahalarta taron, sun jaddada bukatar ci gaba da sanya ido a fannin, musamman domin dakile barazanar rashin samar da jinsin dabbobin a kasar da kuma faduwar darajar fannin.

Shi ma a nasa jawabin a wajen taron, Shugaban aikin, Dakta   Sanusi Abubakar ya sanar da cewa, samar da sahihan bayanan da ci gaba da sanya ido a fannin, na da matukar muhimmanci.

Abubakar ya kara da cewa, manufar da shirin ke son cimma shi ne, domin a kara habaka samar da tsare-tsare da kuma samar da dauki na dogon zango ga fannnin na kiwon kasar.

Haka zalika, gwamnatin tarayya ta ce; tana kan aikin samar da tsarin da zai bayar da damar samun sahihan bayanai, domin renonon nau’ikan ‘ya’yan dabbobin a kasar.

Kiwo
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Manoma 2,930 Buhun Taki 11,720 A Abuja
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ku Gaggauta Fara Yin Shuka A Kakar Bana: Saƙon Hukumar NiMet Ga Manoma
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Fara Aikin Gina Mayankar Zamani A Garin Jos

MASU ALAKA

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Manoma 2,930 Buhun Taki 11,720 A Abuja

June 27, 2026
Kiwo
Noma Da Kiwo

Ku Gaggauta Fara Yin Shuka A Kakar Bana: Saƙon Hukumar NiMet Ga Manoma

June 27, 2026
Kiwo
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Fara Aikin Gina Mayankar Zamani A Garin Jos

June 26, 2026
Next Post
Sace Ɗalibai Ya Karu A Mulkin Tinubu Fiye Da Gwamnatocin Baya – Obi

Sace Ɗalibai Ya Karu A Mulkin Tinubu Fiye Da Gwamnatocin Baya - Obi

LABARAI MASU NASABA

Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Yi Maraba Da Hukuncin Kotu Kan Dakatar Da Jadawalin INEC

June 27, 2026
ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

June 27, 2026
TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

June 27, 2026
Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

June 27, 2026
Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

June 27, 2026
Gasar Kofin Duniya: Senegal Ta Kai Zagaye Na 32 Bayan Lallasa Iraki Da Ci 5-0

Gasar Kofin Duniya: Senegal Ta Kai Zagaye Na 32 Bayan Lallasa Iraki Da Ci 5-0

June 27, 2026
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Shaidar Ɗan Ƙasa, Duba Abin Da Ta Ƙunsa

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Shaidar Ɗan Ƙasa, Duba Abin Da Ta Ƙunsa

June 27, 2026
Kiwo

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 27, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

An Kama Uwa Da Abokiyar Burminta Kan Kisan Jariri A Jihar Yobe

June 27, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Manoma 2,930 Buhun Taki 11,720 A Abuja

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.