Gwamnatin tarayya, ta danganta rashin samun sahihan bayanai a matsayin babban ginshikin da ke sanya wa ana ci gaba da samun gibi a fannin kiwon dabbobin kasar.
Ta kara da cewa, matsalar ta fi yin kamari, a bangaren yin reno da kuma tattalin dabbobin, domin kara samar da wadatunsu a fadin kasar baki-daya.
Ministan Ma’aikar Kula da Bunkasa Kiwon Dabbobi, Idi Mukhtar Maiha, ya yi gargadin cewa; matukar ba a samu cikakkun sahihan bayanai kan renon dabbobin kasar ba, hakan zai yi matukar wuya wajen bunkasawa da kuma ci gaba da samar da jinsin dabbobin a Nijeriya.
Maiha, ya yi wannan gargadin ne a taron bita, domin tattaunawa da masu ruwa da tsaki a Abuja.
Sashen samar da jinsin dabbobi da ke ma’aikata ne ya shirya taron, a karkashin aikin habaka dabbobi da kuma bayar da dauki wato, lPRSP.
“Idan har ba a samar da sahihan bayanan a fannin na kiwon kasar ba, zai yi wuya a iya cimma burin da ake da shi, wajen gano irin nau’in dabbobin da suka dace a yi renonsu, musamman nau’in irin wadanda za su kasance da kowane irin yanayi na shiyyar kasar,” a cewarsa.
Kazaika, mahalarta taron, sun jaddada bukatar ci gaba da sanya ido a fannin, musamman domin dakile barazanar rashin samar da jinsin dabbobin a kasar da kuma faduwar darajar fannin.
Shi ma a nasa jawabin a wajen taron, Shugaban aikin, Dakta Sanusi Abubakar ya sanar da cewa, samar da sahihan bayanan da ci gaba da sanya ido a fannin, na da matukar muhimmanci.
Abubakar ya kara da cewa, manufar da shirin ke son cimma shi ne, domin a kara habaka samar da tsare-tsare da kuma samar da dauki na dogon zango ga fannnin na kiwon kasar.
Haka zalika, gwamnatin tarayya ta ce; tana kan aikin samar da tsarin da zai bayar da damar samun sahihan bayanai, domin renonon nau’ikan ‘ya’yan dabbobin a kasar.














Discussion about this post