ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Nijeriya Na Karbo Bashin Dala Biliyan 12 Daga Kasar Japan

by Abubakar Abba
1 year ago
Japan

Ma’aikatar Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci ta bayyana cewa, ta karbo bashin biliyan 12 na takardar Yen na Kasar Japan, wanda ya yi daidai da dala biliyan 12.

Ministan Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci, Abubakar Kyari ne ya bayyana haka.

  • Yadda Tashar Jirgen Ruwan Apapa-Moniya Za Ta Taimaka Wa Masu Safarar Fitar Da Kaya
  • NIMASA Za Ta Adana Wa Nijeriya Dala Biliyan 400 A Shekara Daga Cazar Kudaden Safarar Kaya

Ya ce, Ma’aikatarsa ta karbo bashin ne daga hukumar bayar da agajin gaggauwa ta kasa da kasa (JICA) da ke Kasar Japan.

ADVERTISEMENT

Kazalika, ma’aikatar ta kuma yabawa hukumar kan goyon bayan da take bai wa Nijeriya.

Ya sanar da cewa, Nijeriya za ta yi amfani da bashin ne, wajen kara habakawa da kuma ciyar da shirin bunkasa aikin noma na kasar nan, wato NAGS-AP.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Ministan Ma’aikatar Aikin Gona da Samar da Wadaccen Abinci, Sanata Abubakar Kayri ne ya bayyana a haka, a cikin sanarwar da ma’aikatar ta fitar.

“Mun samar da tsarin samar da wadataccen abinci a kasar nan, wanda kowanne dan kasar zai amfana da shi”, in ji Kyari.

Daga cikin manyan abubuwan da suka hada da bashin sun hada da; samar da ingantaccen Irin Shinkafa da kuma habaka yadda ake samar da Irin na Shinkafar.

Sauran sun hada da mayar da hankali wajen yin girbin mai kyau, samar da nau’ikan Shinkafar da ke jurewa kowacce irin cutar da ke lalata Irin Shinkafar da aka shuka, aka ajiye a cibiyar gudanar da bincike kan amfanin gona (NCRI) da ke yankin Badeggi a Jihar Neja.

Kazalika, akwai kuma bukatar kara bunkasa kayan aikin gona, inganata aikin malaman gona, amfani da kayan aikin gona na kimiyya domin rika samar da bayanai a kan lokaci, musamman wanda ya shafi sauyin yanayi, samar da farashin kayan amfanin gona a kasuwa, dakile barkewar kwarin da ke lalata amfanin gona da sauransu.

A nasa jawabin, Karamin Minista a Ma’aikatar Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci, Dakta Abdullahi Sabi Abdullahi, ya bayyana gamsuwar da cewa, shuka ingantaccen Irin noma zai taimaka wajen ciyar da daukacin ‘yan Nijeriya gaba.

Dakta Abudullahi ya kara da cewa, ingantancen Iri shi ne, kashin bayan da zai kawo karshen kalubalen da bangeren samar da wadataccen abinci a kasar.

“Wannan hadaka za ta kara karfafawa, musamman kananan manoma na kasar nan guiwa, ta hanyar yin amfani da aikin karfafa wa kanannan manoma gwiwa, wato SHEP, wanda a yanzu aikin ya karade jihohi 14 na kasar nan”, a cewar Abdullahi.

Kazalika, wannan hadakar ta kasance tamkar cike wani gibi ne a tsakanin gudanar da bincike, yin aiki a aikace tare kuma da samar wa manoman kasar nan kayan aikin gona na zamani da kuma samar musu da ilimin kwarewar da ya kamata a fannin na aikin noma.

Shi kuwa, Darakta Janar na Hukumar, wanda kuma shi ne har ila yau, ya jagoranci tawagar kasar ta Japan, Takao Shimokawa ya bayyana cewa, Hukumar ta JICA da kuma Kasar Japan, sun mayar da hankali wajen ganin an bunkasa bangaren noman Shinkafa a Afirka, musamman ma a Nijeriya, duba da cewa, kasar ta kasance kan gaba wajen noman Shinkafa.

Wannan shirin ya nuna a zahiri irin mayar da hankalin da gwamnatin tarayya da Hukumar JICA suka yi, don kara habaka bangaren samar da wadataccen abinci a kasar nan.

Japan
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.