ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussa Daga Ramadan Na 12: Ƙarfafa Alaƙa Da Alƙur’ani A Ramalana

by Nuhu Ubale Ibrahim
3 months ago
Ramadan

A cikin watan Ramalana muna koyon ƙarfafa alaƙarmu da Alƙur’ani mai girma. Ta yaya ba za mu ƙarfafa wannan alaƙa ba, alhali Allah Maɗaukaki Ya zaɓi wannan wata domin saukar da littafinsa mafi girma? Idan lokaci ya samu daraja saboda Alƙur’ani, to ya dace mu ɗaukaka rayuwarmu ta hanyar komawa gare shi.

Allah Mai Tsarki Ya ce a Suratul Baƙara aya ta (185): “Watan Ramalana shi ne aka saukar da Alƙur’ani a cikinsa, shiriya ne ga mutane, kuma ayoyi ne bayyanannu na shiriya, kuma mai rarrabewa ne tsakanin ƙarya da gaskiya”

  • Darussa Daga Ramadan Na 11: Sauƙi Da Sassauci A Shari’a
  • Darussa Daga Ramadan Na 10: Zumunci Da Tausayi

Wannan aya ta nuna mana darajar Ramalana da kuma darajar Alƙur’ani. Alƙur’ani shiriya ne, yana haskaka duhun zuciya. Bayyanannun hujjoji ne, da suke tabbatar da gaskiya. Kuma Mai rarrabewa ne tsakanin gaskiya da ƙarya, da halal da haram, da kuma haske da duhu.

ADVERTISEMENT

Ramalana wata ne da zukata suke natsuwa, sha’awoyi suke rauni, ruhi kuma yake kusantar Allah. Saboda haka karatun Alƙur’ani a wannan wata yana da wani zaƙi na musamman. Ka ga mutane suna ƙoƙarin kammala shi sau ɗaya ko fiye, suna sauraron tafsiri, suna yawaita tadabburi.

Wannan yanayi yana nuna cewa zuciya tana buƙatar Alƙur’ani fiye da komai. Sai dai wata tambaya ita ce: mene ne ya sa wannan kusanci da Alƙur’ani yake raguwa bayan Ramalana? Ina ma za mu lazimci karatunsa tsawon shekara kamar yadda muke lazimtar karantawa a cikin Ramalana. Domin Alƙur’ani ba na wata guda ba ne; jagora ne na rayuwa baki ɗaya, amma watan Ramalana na daban ne wannan shi ne dalilin.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

Ƙarfafa alaƙa da Alƙur’ani yana nufin abubuwa uku:

1. Karatunsa akai-akai, ko da aya kaɗan ce a rana, amma a dawwama ana yi ba tare da tsallake ba.
2. Tadabburi da fahimta, watau tunani a kan ma’anoni da saƙonnin da yake ɗauke da su.
3. Aiwatarwa ta fuskar aiki da shi, watau a mayar da koyarwarsa aiki a rayuwa. Domin Alƙur’ani ba a saukar da shi domin a karanta shi kawai ba, sai domin a rayu da shi. Idan muka karanta shi ba tare da aiki da shi ba, mun rasa wani ɓangare na hikimar saukar da shi.

Ramalana makaranta ce ta komawa ga Alƙur’ani. Idan muka fita daga wannan wata da alƙawarin cewa ba za mu rabu da littafin Allah ba, to mun samu riba mai girma. Domin duk wanda ya riƙe Alƙur’ani, Alƙur’ani zai ɗaukaka shi.

Allah Ya sanya Alƙur’ani ya zama hasken zukatanmu, ya zama maganin damuwarmu, ya zama jagoran rayuwarmu a duniya da Lahira. Ya sa mu zama daga cikin mutanen Alƙur’ani waɗanda suke mutanensa na musamman. Amin.

Abu Razina Nuhu Ubale Ibrahim Paki

Ramadan
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
Ilimi

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

May 31, 2026
Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
Ilimi

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

May 30, 2026
Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
Next Post
Sin Na Yiwa Dukkanin Kasashe Maraba Da Rungumar Manufar Kafa Kawancen GFGG

Sin Na Yiwa Dukkanin Kasashe Maraba Da Rungumar Manufar Kafa Kawancen GFGG

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.