ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussa Daga Ramadan Na 12: Ƙarfafa Alaƙa Da Alƙur’ani A Ramalana

by Nuhu Ubale Ibrahim
4 months ago
Ramadan

A cikin watan Ramalana muna koyon ƙarfafa alaƙarmu da Alƙur’ani mai girma. Ta yaya ba za mu ƙarfafa wannan alaƙa ba, alhali Allah Maɗaukaki Ya zaɓi wannan wata domin saukar da littafinsa mafi girma? Idan lokaci ya samu daraja saboda Alƙur’ani, to ya dace mu ɗaukaka rayuwarmu ta hanyar komawa gare shi.

Allah Mai Tsarki Ya ce a Suratul Baƙara aya ta (185): “Watan Ramalana shi ne aka saukar da Alƙur’ani a cikinsa, shiriya ne ga mutane, kuma ayoyi ne bayyanannu na shiriya, kuma mai rarrabewa ne tsakanin ƙarya da gaskiya”

  • Darussa Daga Ramadan Na 11: Sauƙi Da Sassauci A Shari’a
  • Darussa Daga Ramadan Na 10: Zumunci Da Tausayi

Wannan aya ta nuna mana darajar Ramalana da kuma darajar Alƙur’ani. Alƙur’ani shiriya ne, yana haskaka duhun zuciya. Bayyanannun hujjoji ne, da suke tabbatar da gaskiya. Kuma Mai rarrabewa ne tsakanin gaskiya da ƙarya, da halal da haram, da kuma haske da duhu.

ADVERTISEMENT

Ramalana wata ne da zukata suke natsuwa, sha’awoyi suke rauni, ruhi kuma yake kusantar Allah. Saboda haka karatun Alƙur’ani a wannan wata yana da wani zaƙi na musamman. Ka ga mutane suna ƙoƙarin kammala shi sau ɗaya ko fiye, suna sauraron tafsiri, suna yawaita tadabburi.

Wannan yanayi yana nuna cewa zuciya tana buƙatar Alƙur’ani fiye da komai. Sai dai wata tambaya ita ce: mene ne ya sa wannan kusanci da Alƙur’ani yake raguwa bayan Ramalana? Ina ma za mu lazimci karatunsa tsawon shekara kamar yadda muke lazimtar karantawa a cikin Ramalana. Domin Alƙur’ani ba na wata guda ba ne; jagora ne na rayuwa baki ɗaya, amma watan Ramalana na daban ne wannan shi ne dalilin.

LABARAI MASU NASABA

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

Ƙarfafa alaƙa da Alƙur’ani yana nufin abubuwa uku:

1. Karatunsa akai-akai, ko da aya kaɗan ce a rana, amma a dawwama ana yi ba tare da tsallake ba.
2. Tadabburi da fahimta, watau tunani a kan ma’anoni da saƙonnin da yake ɗauke da su.
3. Aiwatarwa ta fuskar aiki da shi, watau a mayar da koyarwarsa aiki a rayuwa. Domin Alƙur’ani ba a saukar da shi domin a karanta shi kawai ba, sai domin a rayu da shi. Idan muka karanta shi ba tare da aiki da shi ba, mun rasa wani ɓangare na hikimar saukar da shi.

Ramalana makaranta ce ta komawa ga Alƙur’ani. Idan muka fita daga wannan wata da alƙawarin cewa ba za mu rabu da littafin Allah ba, to mun samu riba mai girma. Domin duk wanda ya riƙe Alƙur’ani, Alƙur’ani zai ɗaukaka shi.

Allah Ya sanya Alƙur’ani ya zama hasken zukatanmu, ya zama maganin damuwarmu, ya zama jagoran rayuwarmu a duniya da Lahira. Ya sa mu zama daga cikin mutanen Alƙur’ani waɗanda suke mutanensa na musamman. Amin.

Abu Razina Nuhu Ubale Ibrahim Paki

Ramadan
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Ilimi

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026
ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
Ilimi

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

July 3, 2026
Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa
Fatawa

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

June 21, 2026
Next Post
Sin Na Yiwa Dukkanin Kasashe Maraba Da Rungumar Manufar Kafa Kawancen GFGG

Sin Na Yiwa Dukkanin Kasashe Maraba Da Rungumar Manufar Kafa Kawancen GFGG

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.