ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussa Daga Ramadan Na 12: Ƙarfafa Alaƙa Da Alƙur’ani A Ramalana

by Nuhu Ubale Ibrahim
6 months ago
Ramadan

A cikin watan Ramalana muna koyon ƙarfafa alaƙarmu da Alƙur’ani mai girma. Ta yaya ba za mu ƙarfafa wannan alaƙa ba, alhali Allah Maɗaukaki Ya zaɓi wannan wata domin saukar da littafinsa mafi girma? Idan lokaci ya samu daraja saboda Alƙur’ani, to ya dace mu ɗaukaka rayuwarmu ta hanyar komawa gare shi.

Allah Mai Tsarki Ya ce a Suratul Baƙara aya ta (185): “Watan Ramalana shi ne aka saukar da Alƙur’ani a cikinsa, shiriya ne ga mutane, kuma ayoyi ne bayyanannu na shiriya, kuma mai rarrabewa ne tsakanin ƙarya da gaskiya”

  • Darussa Daga Ramadan Na 11: Sauƙi Da Sassauci A Shari’a
  • Darussa Daga Ramadan Na 10: Zumunci Da Tausayi

Wannan aya ta nuna mana darajar Ramalana da kuma darajar Alƙur’ani. Alƙur’ani shiriya ne, yana haskaka duhun zuciya. Bayyanannun hujjoji ne, da suke tabbatar da gaskiya. Kuma Mai rarrabewa ne tsakanin gaskiya da ƙarya, da halal da haram, da kuma haske da duhu.

ADVERTISEMENT

Ramalana wata ne da zukata suke natsuwa, sha’awoyi suke rauni, ruhi kuma yake kusantar Allah. Saboda haka karatun Alƙur’ani a wannan wata yana da wani zaƙi na musamman. Ka ga mutane suna ƙoƙarin kammala shi sau ɗaya ko fiye, suna sauraron tafsiri, suna yawaita tadabburi.

Wannan yanayi yana nuna cewa zuciya tana buƙatar Alƙur’ani fiye da komai. Sai dai wata tambaya ita ce: mene ne ya sa wannan kusanci da Alƙur’ani yake raguwa bayan Ramalana? Ina ma za mu lazimci karatunsa tsawon shekara kamar yadda muke lazimtar karantawa a cikin Ramalana. Domin Alƙur’ani ba na wata guda ba ne; jagora ne na rayuwa baki ɗaya, amma watan Ramalana na daban ne wannan shi ne dalilin.

LABARAI MASU NASABA

An Tantance Masu Neman Aikin Koyarwa 500 A Jigawa

JAMB Ta Ƙara Wa’adin Amincewar Guraben Karatu Zuwa 30 Satumba

Ƙarfafa alaƙa da Alƙur’ani yana nufin abubuwa uku:

1. Karatunsa akai-akai, ko da aya kaɗan ce a rana, amma a dawwama ana yi ba tare da tsallake ba.
2. Tadabburi da fahimta, watau tunani a kan ma’anoni da saƙonnin da yake ɗauke da su.
3. Aiwatarwa ta fuskar aiki da shi, watau a mayar da koyarwarsa aiki a rayuwa. Domin Alƙur’ani ba a saukar da shi domin a karanta shi kawai ba, sai domin a rayu da shi. Idan muka karanta shi ba tare da aiki da shi ba, mun rasa wani ɓangare na hikimar saukar da shi.

Ramalana makaranta ce ta komawa ga Alƙur’ani. Idan muka fita daga wannan wata da alƙawarin cewa ba za mu rabu da littafin Allah ba, to mun samu riba mai girma. Domin duk wanda ya riƙe Alƙur’ani, Alƙur’ani zai ɗaukaka shi.

Allah Ya sanya Alƙur’ani ya zama hasken zukatanmu, ya zama maganin damuwarmu, ya zama jagoran rayuwarmu a duniya da Lahira. Ya sa mu zama daga cikin mutanen Alƙur’ani waɗanda suke mutanensa na musamman. Amin.

Abu Razina Nuhu Ubale Ibrahim Paki

Ramadan
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Ramadan
Ilimi

An Tantance Masu Neman Aikin Koyarwa 500 A Jigawa

August 31, 2026
Ramadan
Ilimi

JAMB Ta Ƙara Wa’adin Amincewar Guraben Karatu Zuwa 30 Satumba

August 29, 2026
Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa
Ta’aziyya

Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa

August 2, 2026
Next Post
Sin Na Yiwa Dukkanin Kasashe Maraba Da Rungumar Manufar Kafa Kawancen GFGG

Sin Na Yiwa Dukkanin Kasashe Maraba Da Rungumar Manufar Kafa Kawancen GFGG

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.