ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussa Daga Ramadan Na 11: Sauƙi Da Sassauci A Shari’a

by Nuhu Ubale Ibrahim
6 months ago
Ramadan

A cikin watan Ramalana muna koyon sauƙaƙawa da sassautawa a cikin al’amuranmu na yau da kullum, matuƙar hakan ba zai kai zuwa ga saɓon Allah ba.

  • Darussa Daga Ramadan Na 10: Zumunci Da Tausayi
  • Darussa Daga Ramadan Na 9: Danne Fushi Da Nutsuwa A Ramalana

Ramalana, duk da cewa wata ne na ibada mai tsanani, amma a cikinsa ne Allah Ya bayyana mana cewa addinin Musulunci addini ne na sauƙi, ba na tsanani da takura ba. Allah Maɗaukaki Ya ce a cikin Suratul Baƙara aya ta (185): “Allah Yana nufin sauƙi a gare ku, kuma ba Ya nufin tsanani a gare ku” Wannan aya ta zo ne a tsakiyar hukunce-hukuncen azumi, wadda ibada ce mai ɗauke da yunwa da ƙishirwa. Amma duk da haka, Allah Ya bayar da rangwame ga marasa lafiya, da matafiyi, da waɗanda ba za su iya ba.

Wannan yana nuna cewa shari’a ba ta zo domin wahalar da bawa ba, sai dai domin gyara shi da ɗora shi a bisa turbar rahama. Haka kuma, Manzon Allah (SAW) ya kasance abin koyi a wannan fanni. Ya zo a cikin Sahihul Bukhari cewa: “Ba a taɓa ba wa Manzon Allah zaɓi a tsakanin al’amura biyu ba, face ya zaɓi mafi sauƙi a cikinsu, matuƙar ba saɓo ba ne. Idan kuwa saɓo ne, to, shi ne ya fi kowa guje masa”

ADVERTISEMENT

Wannan hadisi yana koya mana daidaito. Sauƙi a Musulunci ba sakaci ba ne, kuma tsanani ba alamar tsoron Allah ba ne. Abin da ake so shi ne bin umarni cikin hikima da sassauci, tare da nisantar abin da Allah Ya hana.

Ramalana yana koya mana cewa; addini ba ya hana sauƙi idan yana cikin halal. Sassauci yana daga cikin halayen Annabi (SAW).

LABARAI MASU NASABA

An Tantance Masu Neman Aikin Koyarwa 500 A Jigawa

JAMB Ta Ƙara Wa’adin Amincewar Guraben Karatu Zuwa 30 Satumba

Tsanani da ƙuntatawa kai ko mutane ba su ne ma’aunin ibada ba. A wasu lokuta mutum yana ɗaukar tsanani a matsayin ƙarfi a addini, alhali kuwa sauƙi da sassauci su ne mafi kusanci da sunnar Annabi (SAW) a gida, da wurin aiki, da cikin mu’amala da al’umma, idan muka riƙe wannan ka’ida, to, mu riƙa zaɓar abu mafi sauƙi muddin ba saɓo ba ne, yin haka zai sanya mu samu kwanciyar hankali da daidaito.

Sai dai a lura, sauƙi ba ya nufin wuce gona da iri ko sakaci. Idan al’amari ya kai ga saɓo, to mumini ya fi kowa nisantar sa. Wannan shi ne mizani na gaskiya, sassauci cikin abin da yake halal, tsayuwa daram a kan nisantar haram.

Idan muka fahimci wannan darasi daga Ramalana, to rayuwarmu za ta zama mai sauƙi, zuciyarmu za ta samu natsuwa, kuma hulɗarmu da mutane za ta inganta.

Allah Ya sa mu kasance masu fahimtar sauƙin addini, masu bin sunnar Annabi (SAW) cikin hikima, Ya kuma tsare mu daga tsanani da sakaci. Amin.

Abu Razina Nuhu Ubale Ibrahim Paki

Ramadan
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Ramadan
Ilimi

An Tantance Masu Neman Aikin Koyarwa 500 A Jigawa

August 31, 2026
Ramadan
Ilimi

JAMB Ta Ƙara Wa’adin Amincewar Guraben Karatu Zuwa 30 Satumba

August 29, 2026
Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa
Ta’aziyya

Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa

August 2, 2026
Next Post
Za A Gudanar Da Zaman Taron Shekara-Shekara Na CPPCC Daga Ranar 4 Zuwa 11 Ga Maris

Za A Gudanar Da Zaman Taron Shekara-Shekara Na CPPCC Daga Ranar 4 Zuwa 11 Ga Maris

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.