ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussa Daga Ramadan Na 11: Sauƙi Da Sassauci A Shari’a

by Nuhu Ubale Ibrahim
4 months ago
Ramadan

A cikin watan Ramalana muna koyon sauƙaƙawa da sassautawa a cikin al’amuranmu na yau da kullum, matuƙar hakan ba zai kai zuwa ga saɓon Allah ba.

  • Darussa Daga Ramadan Na 10: Zumunci Da Tausayi
  • Darussa Daga Ramadan Na 9: Danne Fushi Da Nutsuwa A Ramalana

Ramalana, duk da cewa wata ne na ibada mai tsanani, amma a cikinsa ne Allah Ya bayyana mana cewa addinin Musulunci addini ne na sauƙi, ba na tsanani da takura ba. Allah Maɗaukaki Ya ce a cikin Suratul Baƙara aya ta (185): “Allah Yana nufin sauƙi a gare ku, kuma ba Ya nufin tsanani a gare ku” Wannan aya ta zo ne a tsakiyar hukunce-hukuncen azumi, wadda ibada ce mai ɗauke da yunwa da ƙishirwa. Amma duk da haka, Allah Ya bayar da rangwame ga marasa lafiya, da matafiyi, da waɗanda ba za su iya ba.

Wannan yana nuna cewa shari’a ba ta zo domin wahalar da bawa ba, sai dai domin gyara shi da ɗora shi a bisa turbar rahama. Haka kuma, Manzon Allah (SAW) ya kasance abin koyi a wannan fanni. Ya zo a cikin Sahihul Bukhari cewa: “Ba a taɓa ba wa Manzon Allah zaɓi a tsakanin al’amura biyu ba, face ya zaɓi mafi sauƙi a cikinsu, matuƙar ba saɓo ba ne. Idan kuwa saɓo ne, to, shi ne ya fi kowa guje masa”

ADVERTISEMENT

Wannan hadisi yana koya mana daidaito. Sauƙi a Musulunci ba sakaci ba ne, kuma tsanani ba alamar tsoron Allah ba ne. Abin da ake so shi ne bin umarni cikin hikima da sassauci, tare da nisantar abin da Allah Ya hana.

Ramalana yana koya mana cewa; addini ba ya hana sauƙi idan yana cikin halal. Sassauci yana daga cikin halayen Annabi (SAW).

LABARAI MASU NASABA

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

Tsanani da ƙuntatawa kai ko mutane ba su ne ma’aunin ibada ba. A wasu lokuta mutum yana ɗaukar tsanani a matsayin ƙarfi a addini, alhali kuwa sauƙi da sassauci su ne mafi kusanci da sunnar Annabi (SAW) a gida, da wurin aiki, da cikin mu’amala da al’umma, idan muka riƙe wannan ka’ida, to, mu riƙa zaɓar abu mafi sauƙi muddin ba saɓo ba ne, yin haka zai sanya mu samu kwanciyar hankali da daidaito.

Sai dai a lura, sauƙi ba ya nufin wuce gona da iri ko sakaci. Idan al’amari ya kai ga saɓo, to mumini ya fi kowa nisantar sa. Wannan shi ne mizani na gaskiya, sassauci cikin abin da yake halal, tsayuwa daram a kan nisantar haram.

Idan muka fahimci wannan darasi daga Ramalana, to rayuwarmu za ta zama mai sauƙi, zuciyarmu za ta samu natsuwa, kuma hulɗarmu da mutane za ta inganta.

Allah Ya sa mu kasance masu fahimtar sauƙin addini, masu bin sunnar Annabi (SAW) cikin hikima, Ya kuma tsare mu daga tsanani da sakaci. Amin.

Abu Razina Nuhu Ubale Ibrahim Paki

Ramadan
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
Ilimi

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

July 3, 2026
Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa
Fatawa

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

June 21, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Next Post
Za A Gudanar Da Zaman Taron Shekara-Shekara Na CPPCC Daga Ranar 4 Zuwa 11 Ga Maris

Za A Gudanar Da Zaman Taron Shekara-Shekara Na CPPCC Daga Ranar 4 Zuwa 11 Ga Maris

LABARAI MASU NASABA

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

July 4, 2026
Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.