ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussa Daga Ramadan Na 5: Tsare Gaɓɓai Daga Saɓo

by Nuhu Ubale Ibrahim
4 months ago
Darussa

A cikin watan Ramalana muna koyon cewa za mu iya tsare gaɓɓanmu daga saɓon Allah domin bauta gare Shi, kamar yadda muke kame bakunanmu daga ci da sha saboda umarninsa. Idan mutum zai iya barin abin da yake so kuma yake buƙata kamar abinci da ruwan sha saboda Allah, to lallai zai iya barin saɓo saboda Allah.

Azumi ba wai yunwa da ƙishirwa kaɗai ba ne. A zahiri, yunwa da ƙishirwa horo ne ga zuciya domin ta koyi biyayya. Haƙiƙanin azumi shi ne azumin zuciya da gaɓɓai, azumin harshe daga ƙarya da gulma, azumin ido daga kallon haram, azumin kunne daga sauraron abin da bai dace ba, da azumin zuciya daga hassada da ƙiyayya. Manzon Allah (S.A.W) ya yi gargaɗi mai tsanani game da wannan ma’ana a cikin hadisin da imamul Bukhari ya ruwaito a Sahihinsa inda ya ce: “Duk wanda bai bar zuƙitamalli da aiki da ita ba, to, Allah ba Shi da buƙatar ya bar cinsa da shansa”

  • Darussa Daga Ramadan Na (3)
  • Darussa Daga Ramadan Na (4)

Wannan hadisi yana nuna cewa Allah ba Ya nufin wahalar jikin bawa kawai, amma Yana nufin gyaran hali da zuciya. Idan azumi bai hana mutum ƙarya ba, bai hana shi zalunci ba, bai hana shi gulma da cin mutunci ba, to ya rasa muhimmin ginshiƙin azumi.

ADVERTISEMENT

Ramalana makaranta ce ta horar da kai. Idan mutum zai iya kame kansa daga halal saboda Allah, to me ya sa ba zai kame kansa daga haram ba? Wannan shi ne darasin da ya kamata ya zauna a zuciya.

A zahiri, sau da yawa mutane suna kula da azumin ciki fiye da azumin gaɓɓai. Za ka ga mutum yana tsananin kiyaye bakinsa da cikinsa kada ya sha ruwa ko ya ci abinci, amma ba ya kula da abin da harshensa yake furtawa ko abin da idonsa yake kallo. Wannan kuskure ne a fahimtar azumi.

LABARAI MASU NASABA

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

Azumi yana gina taƙawa a zuciya. Kuma taƙawa ita ce ka bar abin da Allah Ya hana ka, a fili da ɓoye. Idan azumi ya kammala zuciya da halaye, to bayan Ramalana mutum zai zama mai kiyaye dokokin Allah a sauran watanni. Saboda haka, mu sanya Ramalana ya zama wata na tsarkake gaɓɓai. Mu tsare harshenmu, mu kiyaye idanunmu, mu tsarkake zukatanmu. Mu tuna cewa Allah Yana kallon mu a kowane hali.

Allah Ya sa azuminmu ya zama azumin da ya haɗa jiki da zuciya, Ya tsare mu daga saɓo a bayyane da a ɓoye, Ya kuma sanya mu cikin bayinsa masu tsoron Sa. Amin.

Darussa
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa
Fatawa

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

June 21, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
Ilimi

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026
Next Post
Wang Yi Ya Halarci Taron Manyan Jami’ai Karo Na 61 Na Kwamitin Kare Hakkin Dan Adam Na MDD

Wang Yi Ya Halarci Taron Manyan Jami’ai Karo Na 61 Na Kwamitin Kare Hakkin Dan Adam Na MDD

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.