A cikin watan Ramalana muna koyon cewa za mu iya tsare gaɓɓanmu daga saɓon Allah domin bauta gare Shi, kamar yadda muke kame bakunanmu daga ci da sha saboda umarninsa. Idan mutum zai iya barin abin da yake so kuma yake buƙata kamar abinci da ruwan sha saboda Allah, to lallai zai iya barin saɓo saboda Allah.
Azumi ba wai yunwa da ƙishirwa kaɗai ba ne. A zahiri, yunwa da ƙishirwa horo ne ga zuciya domin ta koyi biyayya. Haƙiƙanin azumi shi ne azumin zuciya da gaɓɓai, azumin harshe daga ƙarya da gulma, azumin ido daga kallon haram, azumin kunne daga sauraron abin da bai dace ba, da azumin zuciya daga hassada da ƙiyayya. Manzon Allah (S.A.W) ya yi gargaɗi mai tsanani game da wannan ma’ana a cikin hadisin da imamul Bukhari ya ruwaito a Sahihinsa inda ya ce: “Duk wanda bai bar zuƙitamalli da aiki da ita ba, to, Allah ba Shi da buƙatar ya bar cinsa da shansa”
Wannan hadisi yana nuna cewa Allah ba Ya nufin wahalar jikin bawa kawai, amma Yana nufin gyaran hali da zuciya. Idan azumi bai hana mutum ƙarya ba, bai hana shi zalunci ba, bai hana shi gulma da cin mutunci ba, to ya rasa muhimmin ginshiƙin azumi.
Ramalana makaranta ce ta horar da kai. Idan mutum zai iya kame kansa daga halal saboda Allah, to me ya sa ba zai kame kansa daga haram ba? Wannan shi ne darasin da ya kamata ya zauna a zuciya.
A zahiri, sau da yawa mutane suna kula da azumin ciki fiye da azumin gaɓɓai. Za ka ga mutum yana tsananin kiyaye bakinsa da cikinsa kada ya sha ruwa ko ya ci abinci, amma ba ya kula da abin da harshensa yake furtawa ko abin da idonsa yake kallo. Wannan kuskure ne a fahimtar azumi.
Azumi yana gina taƙawa a zuciya. Kuma taƙawa ita ce ka bar abin da Allah Ya hana ka, a fili da ɓoye. Idan azumi ya kammala zuciya da halaye, to bayan Ramalana mutum zai zama mai kiyaye dokokin Allah a sauran watanni. Saboda haka, mu sanya Ramalana ya zama wata na tsarkake gaɓɓai. Mu tsare harshenmu, mu kiyaye idanunmu, mu tsarkake zukatanmu. Mu tuna cewa Allah Yana kallon mu a kowane hali.
Allah Ya sa azuminmu ya zama azumin da ya haɗa jiki da zuciya, Ya tsare mu daga saɓo a bayyane da a ɓoye, Ya kuma sanya mu cikin bayinsa masu tsoron Sa. Amin.















Discussion about this post