ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussa Daga Ramadan Na 9: Danne Fushi Da Nutsuwa A Ramalana

by Nuhu Ubale Ibrahim
5 months ago
Ramadan

A cikin watan Ramalana muna koyon yadda za mu danne zukatanmu daga abin da ya sosa su, mu shawo kan fushi, mu kuma mallaki kanmu a lokacin da ake tsokanar mu. Domin mutum yana ƙara hikima, da dattako, da kwarjini da kwanciyar hankali idan yana cikin nutsuwa.

Azumi ba horon ciki kaɗai ba ne, horo ne na zuciya da hali. Yana koya mana sarrafa motsin rai, musamman fushi. Sau da yawa fushi yana sa mutum ya faɗi kalmomin da zai yi nadama daga baya, ko ya aikata abin da zai lalata dangantakarsa da mutane. Amma Ramalana yana tsayar da mumini a kan turbar natsuwa da tunani da haƙuri.

  • Darussa Daga Ramadan Na 8: Haƙuri Da Sadaukarwa Domin Rabauta Ta Har Abada
  • Darussa Daga Ramadan Na 7: Farin Ciki Na Gaskiya A Rayuwar Mumini

Manzon Allah (S.A.W) ya koyar da mu wannan tarbiyya a fili. Ya zo a cikin Sahihul Bukhari da Sahihu Muslim cewa ya ce: “dan ɗayanku yana azumi, kada ya yi maganar banza ko wauta, kuma kada ya yi hayaniya ko sa-in-sa. Idan wani ya zage shi ko ya takale shi da faɗa, to, sai ya ce: ‘Ni azumi nake yi’” Wannan umarni yana da ɗauke da hikima mai girma. Ba wai kawai ka yi shiru ba, har ma ka tuna wa kanka cewa kana cikin ibada. Ka tuna cewa kana azumi domin Allah, don haka; ba za ka bari fushi ya ɓata maka ibada ba.
Fadin “Ni azumi nake yi” yana da ma’ana biyu:
1. Tunatawa kanka cewa kana cikin ibada, don haka; sai ka kame zuciyarka.
2. Kana bayar da saƙo ga wanda ya tsokane ka cewa ba ka shirya shiga rikici ba a wannan lokaci.

ADVERTISEMENT

Wannan shi ne matakin dattako. Domin wanda ya iya danne fushi, ya fi ƙarfin wanda ya iya rinjayar mutane da ƙarfi. A hakika, ƙarfi na gaskiya ba ƙarfin jiki ba ne, sai dai ƙarfin mallakar zuciya da sarrafa ta cikin hikima.

Ramalana yana gina wa mumini halin juriya da natsuwa. Idan muka iya danne zukatanmu a cikin azumi, to za mu iya yin hakan bayan Ramalana. Za mu iya zama masu haƙuri a gida, masu natsuwa a wurin aiki, masu kamun kai a cikin al’umma.
Danne zuciya ba rauni ba ne; alama ce ta kamalar tunani da dattako. Natsuwa ba gazawa ba ce; alamar hikima ce. Kuma kwanciyar hankali ba kasala ba ce; alamar cikakken imani ce. Saboda haka, mu sanya Ramalana ya zama wata na gyaran hali. Idan an tsokane mu, mu yi shiru. Idan an ɓata mana rai, mu nemi lada a wurin Allah. Idan aka neme mu da faɗa, to mu zaɓi zaman lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

Allah Ya ba mu ikon danne zukatanmu daga fushi, Ya kawata mu da halin natsuwa da hikima, Ya kuma karɓi azuminmu cikin yardarsa. Amin.

Abu Razina Nuhu Ubale Ibrahim Paki

Ramadan
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Ilimi

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026
ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
Ilimi

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

July 3, 2026
Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa
Fatawa

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

June 21, 2026
Next Post
Zaɓen Ƙananan Hukumomin Abuja Ya Bar Baya Da Ƙura

Zaɓen Ƙananan Hukumomin Abuja Ya Bar Baya Da Ƙura

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.