ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussa Daga Ramadan Na 9: Danne Fushi Da Nutsuwa A Ramalana

by Nuhu Ubale Ibrahim
4 months ago
Ramadan

A cikin watan Ramalana muna koyon yadda za mu danne zukatanmu daga abin da ya sosa su, mu shawo kan fushi, mu kuma mallaki kanmu a lokacin da ake tsokanar mu. Domin mutum yana ƙara hikima, da dattako, da kwarjini da kwanciyar hankali idan yana cikin nutsuwa.

Azumi ba horon ciki kaɗai ba ne, horo ne na zuciya da hali. Yana koya mana sarrafa motsin rai, musamman fushi. Sau da yawa fushi yana sa mutum ya faɗi kalmomin da zai yi nadama daga baya, ko ya aikata abin da zai lalata dangantakarsa da mutane. Amma Ramalana yana tsayar da mumini a kan turbar natsuwa da tunani da haƙuri.

  • Darussa Daga Ramadan Na 8: Haƙuri Da Sadaukarwa Domin Rabauta Ta Har Abada
  • Darussa Daga Ramadan Na 7: Farin Ciki Na Gaskiya A Rayuwar Mumini

Manzon Allah (S.A.W) ya koyar da mu wannan tarbiyya a fili. Ya zo a cikin Sahihul Bukhari da Sahihu Muslim cewa ya ce: “dan ɗayanku yana azumi, kada ya yi maganar banza ko wauta, kuma kada ya yi hayaniya ko sa-in-sa. Idan wani ya zage shi ko ya takale shi da faɗa, to, sai ya ce: ‘Ni azumi nake yi’” Wannan umarni yana da ɗauke da hikima mai girma. Ba wai kawai ka yi shiru ba, har ma ka tuna wa kanka cewa kana cikin ibada. Ka tuna cewa kana azumi domin Allah, don haka; ba za ka bari fushi ya ɓata maka ibada ba.
Fadin “Ni azumi nake yi” yana da ma’ana biyu:
1. Tunatawa kanka cewa kana cikin ibada, don haka; sai ka kame zuciyarka.
2. Kana bayar da saƙo ga wanda ya tsokane ka cewa ba ka shirya shiga rikici ba a wannan lokaci.

ADVERTISEMENT

Wannan shi ne matakin dattako. Domin wanda ya iya danne fushi, ya fi ƙarfin wanda ya iya rinjayar mutane da ƙarfi. A hakika, ƙarfi na gaskiya ba ƙarfin jiki ba ne, sai dai ƙarfin mallakar zuciya da sarrafa ta cikin hikima.

Ramalana yana gina wa mumini halin juriya da natsuwa. Idan muka iya danne zukatanmu a cikin azumi, to za mu iya yin hakan bayan Ramalana. Za mu iya zama masu haƙuri a gida, masu natsuwa a wurin aiki, masu kamun kai a cikin al’umma.
Danne zuciya ba rauni ba ne; alama ce ta kamalar tunani da dattako. Natsuwa ba gazawa ba ce; alamar hikima ce. Kuma kwanciyar hankali ba kasala ba ce; alamar cikakken imani ce. Saboda haka, mu sanya Ramalana ya zama wata na gyaran hali. Idan an tsokane mu, mu yi shiru. Idan an ɓata mana rai, mu nemi lada a wurin Allah. Idan aka neme mu da faɗa, to mu zaɓi zaman lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

Allah Ya ba mu ikon danne zukatanmu daga fushi, Ya kawata mu da halin natsuwa da hikima, Ya kuma karɓi azuminmu cikin yardarsa. Amin.

Abu Razina Nuhu Ubale Ibrahim Paki

Ramadan
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa
Fatawa

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

June 21, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
Ilimi

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026
Next Post
Zaɓen Ƙananan Hukumomin Abuja Ya Bar Baya Da Ƙura

Zaɓen Ƙananan Hukumomin Abuja Ya Bar Baya Da Ƙura

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.