ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussa Daga Ramadan Na 9: Danne Fushi Da Nutsuwa A Ramalana

by Nuhu Ubale Ibrahim
6 months ago
Ramadan

A cikin watan Ramalana muna koyon yadda za mu danne zukatanmu daga abin da ya sosa su, mu shawo kan fushi, mu kuma mallaki kanmu a lokacin da ake tsokanar mu. Domin mutum yana ƙara hikima, da dattako, da kwarjini da kwanciyar hankali idan yana cikin nutsuwa.

Azumi ba horon ciki kaɗai ba ne, horo ne na zuciya da hali. Yana koya mana sarrafa motsin rai, musamman fushi. Sau da yawa fushi yana sa mutum ya faɗi kalmomin da zai yi nadama daga baya, ko ya aikata abin da zai lalata dangantakarsa da mutane. Amma Ramalana yana tsayar da mumini a kan turbar natsuwa da tunani da haƙuri.

  • Darussa Daga Ramadan Na 8: Haƙuri Da Sadaukarwa Domin Rabauta Ta Har Abada
  • Darussa Daga Ramadan Na 7: Farin Ciki Na Gaskiya A Rayuwar Mumini

Manzon Allah (S.A.W) ya koyar da mu wannan tarbiyya a fili. Ya zo a cikin Sahihul Bukhari da Sahihu Muslim cewa ya ce: “dan ɗayanku yana azumi, kada ya yi maganar banza ko wauta, kuma kada ya yi hayaniya ko sa-in-sa. Idan wani ya zage shi ko ya takale shi da faɗa, to, sai ya ce: ‘Ni azumi nake yi’” Wannan umarni yana da ɗauke da hikima mai girma. Ba wai kawai ka yi shiru ba, har ma ka tuna wa kanka cewa kana cikin ibada. Ka tuna cewa kana azumi domin Allah, don haka; ba za ka bari fushi ya ɓata maka ibada ba.
Fadin “Ni azumi nake yi” yana da ma’ana biyu:
1. Tunatawa kanka cewa kana cikin ibada, don haka; sai ka kame zuciyarka.
2. Kana bayar da saƙo ga wanda ya tsokane ka cewa ba ka shirya shiga rikici ba a wannan lokaci.

ADVERTISEMENT

Wannan shi ne matakin dattako. Domin wanda ya iya danne fushi, ya fi ƙarfin wanda ya iya rinjayar mutane da ƙarfi. A hakika, ƙarfi na gaskiya ba ƙarfin jiki ba ne, sai dai ƙarfin mallakar zuciya da sarrafa ta cikin hikima.

Ramalana yana gina wa mumini halin juriya da natsuwa. Idan muka iya danne zukatanmu a cikin azumi, to za mu iya yin hakan bayan Ramalana. Za mu iya zama masu haƙuri a gida, masu natsuwa a wurin aiki, masu kamun kai a cikin al’umma.
Danne zuciya ba rauni ba ne; alama ce ta kamalar tunani da dattako. Natsuwa ba gazawa ba ce; alamar hikima ce. Kuma kwanciyar hankali ba kasala ba ce; alamar cikakken imani ce. Saboda haka, mu sanya Ramalana ya zama wata na gyaran hali. Idan an tsokane mu, mu yi shiru. Idan an ɓata mana rai, mu nemi lada a wurin Allah. Idan aka neme mu da faɗa, to mu zaɓi zaman lafiya.

LABARAI MASU NASABA

An Tantance Masu Neman Aikin Koyarwa 500 A Jigawa

JAMB Ta Ƙara Wa’adin Amincewar Guraben Karatu Zuwa 30 Satumba

Allah Ya ba mu ikon danne zukatanmu daga fushi, Ya kawata mu da halin natsuwa da hikima, Ya kuma karɓi azuminmu cikin yardarsa. Amin.

Abu Razina Nuhu Ubale Ibrahim Paki

Ramadan
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Ramadan
Ilimi

An Tantance Masu Neman Aikin Koyarwa 500 A Jigawa

August 31, 2026
Ramadan
Ilimi

JAMB Ta Ƙara Wa’adin Amincewar Guraben Karatu Zuwa 30 Satumba

August 29, 2026
Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa
Ta’aziyya

Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa

August 2, 2026
Next Post
Zaɓen Ƙananan Hukumomin Abuja Ya Bar Baya Da Ƙura

Zaɓen Ƙananan Hukumomin Abuja Ya Bar Baya Da Ƙura

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.