ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussa Daga Ramadan Na 9: Danne Fushi Da Nutsuwa A Ramalana

by Nuhu Ubale Ibrahim
3 months ago
Ramadan

A cikin watan Ramalana muna koyon yadda za mu danne zukatanmu daga abin da ya sosa su, mu shawo kan fushi, mu kuma mallaki kanmu a lokacin da ake tsokanar mu. Domin mutum yana ƙara hikima, da dattako, da kwarjini da kwanciyar hankali idan yana cikin nutsuwa.

Azumi ba horon ciki kaɗai ba ne, horo ne na zuciya da hali. Yana koya mana sarrafa motsin rai, musamman fushi. Sau da yawa fushi yana sa mutum ya faɗi kalmomin da zai yi nadama daga baya, ko ya aikata abin da zai lalata dangantakarsa da mutane. Amma Ramalana yana tsayar da mumini a kan turbar natsuwa da tunani da haƙuri.

  • Darussa Daga Ramadan Na 8: Haƙuri Da Sadaukarwa Domin Rabauta Ta Har Abada
  • Darussa Daga Ramadan Na 7: Farin Ciki Na Gaskiya A Rayuwar Mumini

Manzon Allah (S.A.W) ya koyar da mu wannan tarbiyya a fili. Ya zo a cikin Sahihul Bukhari da Sahihu Muslim cewa ya ce: “dan ɗayanku yana azumi, kada ya yi maganar banza ko wauta, kuma kada ya yi hayaniya ko sa-in-sa. Idan wani ya zage shi ko ya takale shi da faɗa, to, sai ya ce: ‘Ni azumi nake yi’” Wannan umarni yana da ɗauke da hikima mai girma. Ba wai kawai ka yi shiru ba, har ma ka tuna wa kanka cewa kana cikin ibada. Ka tuna cewa kana azumi domin Allah, don haka; ba za ka bari fushi ya ɓata maka ibada ba.
Fadin “Ni azumi nake yi” yana da ma’ana biyu:
1. Tunatawa kanka cewa kana cikin ibada, don haka; sai ka kame zuciyarka.
2. Kana bayar da saƙo ga wanda ya tsokane ka cewa ba ka shirya shiga rikici ba a wannan lokaci.

ADVERTISEMENT

Wannan shi ne matakin dattako. Domin wanda ya iya danne fushi, ya fi ƙarfin wanda ya iya rinjayar mutane da ƙarfi. A hakika, ƙarfi na gaskiya ba ƙarfin jiki ba ne, sai dai ƙarfin mallakar zuciya da sarrafa ta cikin hikima.

Ramalana yana gina wa mumini halin juriya da natsuwa. Idan muka iya danne zukatanmu a cikin azumi, to za mu iya yin hakan bayan Ramalana. Za mu iya zama masu haƙuri a gida, masu natsuwa a wurin aiki, masu kamun kai a cikin al’umma.
Danne zuciya ba rauni ba ne; alama ce ta kamalar tunani da dattako. Natsuwa ba gazawa ba ce; alamar hikima ce. Kuma kwanciyar hankali ba kasala ba ce; alamar cikakken imani ce. Saboda haka, mu sanya Ramalana ya zama wata na gyaran hali. Idan an tsokane mu, mu yi shiru. Idan an ɓata mana rai, mu nemi lada a wurin Allah. Idan aka neme mu da faɗa, to mu zaɓi zaman lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

Allah Ya ba mu ikon danne zukatanmu daga fushi, Ya kawata mu da halin natsuwa da hikima, Ya kuma karɓi azuminmu cikin yardarsa. Amin.

Abu Razina Nuhu Ubale Ibrahim Paki

Ramadan
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
Ilimi

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

May 31, 2026
Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
Ilimi

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

May 30, 2026
Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
Next Post
Zaɓen Ƙananan Hukumomin Abuja Ya Bar Baya Da Ƙura

Zaɓen Ƙananan Hukumomin Abuja Ya Bar Baya Da Ƙura

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.