Sama da dawaki 1,000 ake sa ran za su fafata a babbar gasar tseren dawaki na “Premie” da ake gudanarwa a Jihar Kaduna, wadda ta ja hankalin masu sha’awar wasan daga sassa daban-daban na Nijeriya da ma ƙasashe maƙwabta.
An ƙaddamar da gasar ne a filin wasanni na Murtala da ke Kaduna, inda aka ga ɗimbin mahalarta ciki har da masu tsaren dawaki daga jihohi daban-daban na ƙasar nan da kuma wasu daga ƙasashen Nijar da Kamaru.
- Lokacin Cire Jar Hula Bai Yi Ba – Gwamnan Kano
- ’Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 1 Tare Da Sace 11 A Kaduna
Da yake jawabi bayan kammala zagayen farko na gasar, jagoran shirya tseren dawakin, Alhaji Salim Salihu Adam, ya bayyana cewa wannan gasa na da matuƙar muhimmanci wajen ƙarfafa haɗin kai da zumunci tsakanin al’ummomi.
Ya ce, “Wannan gasa ba kawai nishaɗi ba ce, tana kuma taimakawa wajen haɗa kan jama’a daga yankuna daban-daban. Mun yi farin ciki da yadda mahalarta suka fito da yawa, har daga ƙasashen waje.”
Shugaban ya ƙara da cewa, sama da dawaki guda dubu ɗaya ne aka tanadar domin shiga gasar ta bana, abin da ya nuna yadda harkar tseren dawaki ke ci gaba da bunƙasa a yankin arewa da ma ƙasar baki ɗaya.
Gasar dai na ci gaba da jan hankalin masu kallo, inda ake sa ran za a kammala gasar cikin kwanaki masu zuwa, tare da fatan za a samu gagarumar nasara da kuma ƙarin haɗin kai tsakanin mahalarta.















Discussion about this post