Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya amince cewa hauhawar farashin man fetur na jefa ‘yan Nijeriya cikin wahala, amma ya buƙace su da su ci gaba da fatan haƙuri da fatan samun sauƙi, yana mai cewa halin da ake ciki a ƙasar ya fi na wasu ƙasashen Afirka sauƙi.
Tinubu ya bayyana haka ne yayin wata ziyara da ya kai Jihar Bayelsa ranar Juma’a, inda ya je ƙaddamar da muhimman ayyuka. Ya ce gwamnati na sauraron koken jama’a, musamman yadda tsadar mai ke ƙara matsin rayuwa, amma ya buƙaci a duba halin da wasu ƙasashe ke ciki domin a gode wa Allah.
- Fadar Shugaban Ƙasa Ta Gargaɗi Peter Obi Kan Zargin Tinubu Na Haddasa Rikici A ADC
- 2027: Gwamna Ododo Ya Shirya Gangamin Goyon Bayan Tinubu A Kogi
Ya ce, “Haƙiƙa farashin mai na matuƙar tasiri ga rayuwar jama’a, amma idan aka kwatanta da wasu ƙasashe kamar Kenya, ‘yan Nijeriya na cikin sauƙi. Ba za mu ja da baya ba, za mu ci gaba da nemo hanyoyin rage raɗaɗin da talakawa ke fuskanta.”
Shugaban ya tabbatar da cewa gwamnatinsa na nan daram wajen aiwatar da matakan rage tasirin matsalolin tattalin arziƙi, musamman ga masu rauni a cikin al’umma.
Ya kuma jaddada cewa duk da ƙalubalen da ake fuskanta a yanzu, gwamnati za ta ci gaba da aiwatar da gyare-gyare domin daidaita tattalin arziƙi da inganta rayuwar ‘yan ƙasa.















Discussion about this post