ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 29, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Diezani Ta Kashe Fam 140,000 A Kayan Daki Masu Tsada – Kotun Birtaniya

by Rabi'u Ali Indabawa
6 months ago
Diezani

Masu gabatar da kara na Virtaniya sun shaida wa Kotun Southwark Crown da ke London cewa tsohuwar Ministar Albarkatun Man Fetur ta Nijeriya, Diezani Alison-Madueke, ta kashe kusan fam £140,000 wajen sayen kayan daki na alatu da kayan ado a rana guda.

Masu gabatar da karar sun ce wannan kashe-kashen kudi ya faru ne a lokacin da ake zargin Alison-Madueke tana karvar cin hanci (alawus-alawus) daga wasu manyan mutane a masana’antar man fetur.

  • Ka Manta Da Komai, Ka Bar Abba Ya Yi Wa Kano Aiki — Matar Ganduje Ga Kwankwaso
  • NDLEA Ta Yi Alkawarin Kwace Kadarorin Da Ke Ba Da Mafaka Ga Dillalan Kayoyi

A halin yanzu, Alison-Madueke na fuskantar shari’a tare da jagoran kamfanin mai, Olatimvo Ayinde, da kuma dan uwanta, Doye Agama. Mutanen ukun suna fuskantar tuhume-tuhume guda viyar da suka shafi zargin karbar cin hanci. Dukkansu sun musanta laifin da ake zarginsu da shi.

ADVERTISEMENT

A cewar masu gabatar da kara, tsohuwar ministar ta yi wadannan sayayyar ne a wani shagon kayan tarihi na alatu a birnin London, inda ta sayi fitilu na musamman da aka kera bisa oda, kayan daki masu inganci, da kuma ayyukan fasaha na ado.

An shaida wa kotu cewa ana zargin an viya kudin kayan ta hannun wasu tsaka-tsaki, va kai tsaye ta hannun Alison Madueke ba.

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

Lauyar masu gavatar da kara, Alexander Healy, ta fada wa alkalai cewa Alison Madueke “ta rayu cikin rayuwar alatu a London,” inda ta kara da cewa ana zargin wasu ’yan kasuwa da ke neman samun tasiri a harkar man fetur ta Nijeriya ne suka tallafa wa wannan salon rayuwa.

Ta ce ana zargin cin hancin  ba a bayar da shi a matsayin kudi kai tsaye va, sai dai a matsayin kayayyakin alatu da kuma dama ta amfani da kadarori masu tsada.

Tun da farko, a ranar 27 ga Janairu, kotun ta ji cewa ana zargin tsohuwar ministar ta karbi kayayyakin alatu da kuma amfani da manyan kadarorin kasa a matsayin alawus-alawus yayin da take kan mukaminta.

Gidan talabijin na Channels, ya ruwaito cewa magoya baya daga al’ummar Ijaw a Nijeriya sun cika wurin zama na jama’a a kotun, inda da dama daga cikinsu suka yi tafiya zuwa London domin bibiyar shari’ar.

Bangaren kariya ya musanta dukkan zarge-zargen. A ranar 29 ga Janairu, Jonathan Laidlaw, lauyan da ke kare Alison Madueke, ya shaida wa kotu cewa abokiyar aikinsa va ta da cikakken iko kan bayar da kwangilolin man fetur a lokacin da take minista.

Ya yi jayayya cewa Alison Madueke ta yi aiki ne kawai a matsayin “hatimi na tabbatarwa” ga shawarwarin da hukumomi da jami’an da suka dace suka riga suka yanke, yana mai jaddada cewa ba ta yi tasiri wajen bayar da kwangiloli ba, kuma ba ta karɓi cin hanci ba.

Diezani
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kungiya Ta Nemi Mambobinta Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
Kisan Woro A Jihar Kwara Ya Bayyana Rugujewar Tsaron Karkara A Nijeriya — Gbenga Hashim

Kisan Woro A Jihar Kwara Ya Bayyana Rugujewar Tsaron Karkara A Nijeriya — Gbenga Hashim

LABARAI MASU NASABA

Mun Yi Ƙoƙarin Sasanta Iran Da Amurka A Lokacin Gasar Kofin Duniya – Infantino

Mun Yi Ƙoƙarin Sasanta Iran Da Amurka A Lokacin Gasar Kofin Duniya – Infantino

July 29, 2026
Sin Ta Yi Martani Game Da Yiwuwar Kara Kudaden Da Amurka Ke Kashewa Da Nufin Dakile Tasirin Kasar Sin

Sin Ta Yi Martani Game Da Yiwuwar Kara Kudaden Da Amurka Ke Kashewa Da Nufin Dakile Tasirin Kasar Sin

July 29, 2026
Gwamna Sule Ya Halarci Ƙaddamar da Kamfanin Jinlide•Qiangyu New Energy, Ya Ƙara Jaddada Aniyar Jawo Masu Zuba Jari

Gwamna Sule Ya Halarci Ƙaddamar da Kamfanin Jinlide•Qiangyu New Energy, Ya Ƙara Jaddada Aniyar Jawo Masu Zuba Jari

July 29, 2026
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Fitar Da Takarda Game Da Matsayin Sin Kan Abin Da Ake Kira “Samar Da Kayayyaki Fiye Da Kima”

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Fitar Da Takarda Game Da Matsayin Sin Kan Abin Da Ake Kira “Samar Da Kayayyaki Fiye Da Kima”

July 29, 2026
Sana’ar Ƙosai: Remi Tinubu Ta Yi Kira ga Burna Boy da Davido Su Taimaka wa Talakawa

Ba Ma Fatan Wani Ɗan Nijeriya Ya Kwana da Yunwa — Remi Tinubu

July 29, 2026
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Soke Umarnin Cire Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu Huɗu

July 28, 2026
Kayayyaki Masu Fasahar AI Sun Zamo Sabbin Abubuwa Masu Tasiri A Cinikin Waje Na Kasar Sin

Kayayyaki Masu Fasahar AI Sun Zamo Sabbin Abubuwa Masu Tasiri A Cinikin Waje Na Kasar Sin

July 28, 2026
Ruwa

2027: Gwamnan Kaduna Ya Sanar Da Sabon Mataimakinsa A Zaɓen Gwamna

July 28, 2026
Xi Jinping Ya Yi Bayani Kan Ayyuka Masu Nasaba Da Sinawan Dake Ketare

Xi Jinping Ya Yi Bayani Kan Ayyuka Masu Nasaba Da Sinawan Dake Ketare

July 28, 2026
Xi Ya Tattauna Da Shugaban Slovak A Beijing

Xi Ya Tattauna Da Shugaban Slovak A Beijing

July 28, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.