ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Diezani Ta Kashe Fam 140,000 A Kayan Daki Masu Tsada – Kotun Birtaniya

by Rabi'u Ali Indabawa
4 months ago
Diezani

Masu gabatar da kara na Virtaniya sun shaida wa Kotun Southwark Crown da ke London cewa tsohuwar Ministar Albarkatun Man Fetur ta Nijeriya, Diezani Alison-Madueke, ta kashe kusan fam £140,000 wajen sayen kayan daki na alatu da kayan ado a rana guda.

Masu gabatar da karar sun ce wannan kashe-kashen kudi ya faru ne a lokacin da ake zargin Alison-Madueke tana karvar cin hanci (alawus-alawus) daga wasu manyan mutane a masana’antar man fetur.

  • Ka Manta Da Komai, Ka Bar Abba Ya Yi Wa Kano Aiki — Matar Ganduje Ga Kwankwaso
  • NDLEA Ta Yi Alkawarin Kwace Kadarorin Da Ke Ba Da Mafaka Ga Dillalan Kayoyi

A halin yanzu, Alison-Madueke na fuskantar shari’a tare da jagoran kamfanin mai, Olatimvo Ayinde, da kuma dan uwanta, Doye Agama. Mutanen ukun suna fuskantar tuhume-tuhume guda viyar da suka shafi zargin karbar cin hanci. Dukkansu sun musanta laifin da ake zarginsu da shi.

ADVERTISEMENT

A cewar masu gabatar da kara, tsohuwar ministar ta yi wadannan sayayyar ne a wani shagon kayan tarihi na alatu a birnin London, inda ta sayi fitilu na musamman da aka kera bisa oda, kayan daki masu inganci, da kuma ayyukan fasaha na ado.

An shaida wa kotu cewa ana zargin an viya kudin kayan ta hannun wasu tsaka-tsaki, va kai tsaye ta hannun Alison Madueke ba.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

Lauyar masu gavatar da kara, Alexander Healy, ta fada wa alkalai cewa Alison Madueke “ta rayu cikin rayuwar alatu a London,” inda ta kara da cewa ana zargin wasu ’yan kasuwa da ke neman samun tasiri a harkar man fetur ta Nijeriya ne suka tallafa wa wannan salon rayuwa.

Ta ce ana zargin cin hancin  ba a bayar da shi a matsayin kudi kai tsaye va, sai dai a matsayin kayayyakin alatu da kuma dama ta amfani da kadarori masu tsada.

Tun da farko, a ranar 27 ga Janairu, kotun ta ji cewa ana zargin tsohuwar ministar ta karbi kayayyakin alatu da kuma amfani da manyan kadarorin kasa a matsayin alawus-alawus yayin da take kan mukaminta.

Gidan talabijin na Channels, ya ruwaito cewa magoya baya daga al’ummar Ijaw a Nijeriya sun cika wurin zama na jama’a a kotun, inda da dama daga cikinsu suka yi tafiya zuwa London domin bibiyar shari’ar.

Bangaren kariya ya musanta dukkan zarge-zargen. A ranar 29 ga Janairu, Jonathan Laidlaw, lauyan da ke kare Alison Madueke, ya shaida wa kotu cewa abokiyar aikinsa va ta da cikakken iko kan bayar da kwangilolin man fetur a lokacin da take minista.

Ya yi jayayya cewa Alison Madueke ta yi aiki ne kawai a matsayin “hatimi na tabbatarwa” ga shawarwarin da hukumomi da jami’an da suka dace suka riga suka yanke, yana mai jaddada cewa ba ta yi tasiri wajen bayar da kwangiloli ba, kuma ba ta karɓi cin hanci ba.

Diezani
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Iran Ta Yi Wa Sansanonin Sojin Amurka 20 Mummunar Barna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Next Post
Kisan Woro A Jihar Kwara Ya Bayyana Rugujewar Tsaron Karkara A Nijeriya — Gbenga Hashim

Kisan Woro A Jihar Kwara Ya Bayyana Rugujewar Tsaron Karkara A Nijeriya — Gbenga Hashim

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

June 15, 2026
An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026
Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

June 14, 2026
Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

June 14, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

June 14, 2026
An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 14, 2026
Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

June 14, 2026
Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

June 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.