ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Yi Alkawarin Kwace Kadarorin Da Ke Ba Da Mafaka Ga Dillalan Kayoyi

by Rabi'u Ali Indabawa
7 months ago
NDLEA

Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) tare da wata kungiyar farar hula mai suna Eagle Crime Awareness and Prebention Initiatibe (ECAPI) sun yi alkawarin kara kaimi wajen kwace kadarorin da ke da alaka da fataucin kwayoyi, da kuma gidajen da ake amfani da su wajen ba wa dillalan kwayoyi mafaka a fadin Jihar Legas.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da wanda ya kafa kuma shugaban ECAPI, Sam Adams, ya fitar a ranar Talata, wadda PUNCH Metro ta samu.

  • Kasar Sin Na Da Kayayyakin Tarihi Na Halittu Na Duniya Guda 15
  • Sojoji Sun Kashe Ɗan Fashi, Sun Kama Ɓarayin Shanu A Binuwe Da Nasarawa

A cewarsa, an yi wannan alkawari ne a ranar Asabar yayin wani babban gangamin wayar da kai kan yaki da kwayoyi, wanda Kwamitin Dabaru na NDLEA na Jihar Legas ya shirya tare da hadin gwiwar ECAPI, inda hukumomin suka kai gangamin wayar da kan jama’a zuwa manyan yankunan da ake fama da matsalar kwayoyi a jihar.

ADVERTISEMENT

“Kwayoyi na lalata rayuka, lafiya, mafarkai, har ma da tattalin arziki. Mun ayyana dokar rashin juriya gaba daya. Masu gidajen da suka bar a yi amfani da kadarorinsu wajen sayar da kwayoyi su sani cewa irin wadannan kadarori na iya fuskantar kwacewa.

“Gangamin tafiyar wayar da kan ya fara ne daga Maryland, ya bi ta Mushin, Oshodi, Ojuelegba, Costain da Tsibirin Legas, inda jami’an NDLEA da masu sa-kai na ECAPI suka tattauna da mazauna yankuna, matasa, da kuma wadanda ake zargi da amfani da kwayoyi, ta amfani da harsunan gida daban-daban,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

Ya kuma bayyana shirye-shiryen fadada gangamin yaki da kwayoyi zuwa dukkan jihohi 36 na kasar nan da Babban Birnin Tarayya (FCT), inda ya kara da cewa ECAPI za ta ci gaba da aiki tare da hukumomin tsaro domin tabbatar da ci gaba da wannan yunkuri.

Adams ya bayyana hadin gwiwar da NDLEA a matsayin mai amfani kwarai, yana mai lura da cewa an kuma mika irin wannan hadin gwiwa ga sauran hukumomin tsaro da na yaki da cin hanci da rashawa.

A cewar sanarwar, Kwamandan NDLEA na Jihar Legas, Abubakar Wali, yayin gangamin wayar da kai, ya ce hukumar na karfafa dabarun aikinta ta hanyar mayar da hankali kan kwato kudade da kadarorin da aka samu daga laifukan da suka shafi kwayoyi.

Ya jaddada cewa gidajen da ake amfani da su wajen ba wa dillalan kwayoyi mafaka ba za su kara tsira ba, yana mai cewa kwace kadarori wata hanya ce mai karfi ta hana yawaitar laifukan kwayoyi.

Wali ya kara da cewa hukumar na sake ba da muhimmanci ga rigakafi da sauya tunanin al’umma, yana mai bayyana gangamin wayar da kai a tituna a matsayin muhimmin bangare na yaki da kwayoyi.

“Yakinmu bai tsaya kawai akan kama mutane da gurfanar da su a kotu ba. Yanzu muna kai hari kai tsaye ga kadarori. A Legas, mun kwace kudade, otal-otal, gidaje da sauran kadarori da ke da alaka da harkokin kwayoyi, mun kuma mayar da su cikin asusun gwamnati,” in ji shi.

“Wannan tafiyar wayar da kai ba ta zama alama kawai ba. Tana nuna kudurarmu ta fuskantar matsalar shan da fataucin kwayoyi kai tsaye. Kwayoyi na lalata rayuka, iyalai da makomar matasanmu,” ya kara da fada.

Masana sun sha yin kira ga ’yan al’umma da su shiga wannan yaki da shan miyagun kwayoyi, suna jaddada cewa hadin kan kowa da kowa ne kadai zai iya kawo karshen wannan annoba.

NDLEA
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
Garkuwa: TETFund, NSCDC Sun Hada Gwiwa Don Magance Tsaro A Makarantu

Garkuwa: TETFund, NSCDC Sun Hada Gwiwa Don Magance Tsaro A Makarantu

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.