ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Yi Alkawarin Kwace Kadarorin Da Ke Ba Da Mafaka Ga Dillalan Kayoyi

by Rabi'u Ali Indabawa
5 months ago
NDLEA

Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) tare da wata kungiyar farar hula mai suna Eagle Crime Awareness and Prebention Initiatibe (ECAPI) sun yi alkawarin kara kaimi wajen kwace kadarorin da ke da alaka da fataucin kwayoyi, da kuma gidajen da ake amfani da su wajen ba wa dillalan kwayoyi mafaka a fadin Jihar Legas.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da wanda ya kafa kuma shugaban ECAPI, Sam Adams, ya fitar a ranar Talata, wadda PUNCH Metro ta samu.

  • Kasar Sin Na Da Kayayyakin Tarihi Na Halittu Na Duniya Guda 15
  • Sojoji Sun Kashe Ɗan Fashi, Sun Kama Ɓarayin Shanu A Binuwe Da Nasarawa

A cewarsa, an yi wannan alkawari ne a ranar Asabar yayin wani babban gangamin wayar da kai kan yaki da kwayoyi, wanda Kwamitin Dabaru na NDLEA na Jihar Legas ya shirya tare da hadin gwiwar ECAPI, inda hukumomin suka kai gangamin wayar da kan jama’a zuwa manyan yankunan da ake fama da matsalar kwayoyi a jihar.

ADVERTISEMENT

“Kwayoyi na lalata rayuka, lafiya, mafarkai, har ma da tattalin arziki. Mun ayyana dokar rashin juriya gaba daya. Masu gidajen da suka bar a yi amfani da kadarorinsu wajen sayar da kwayoyi su sani cewa irin wadannan kadarori na iya fuskantar kwacewa.

“Gangamin tafiyar wayar da kan ya fara ne daga Maryland, ya bi ta Mushin, Oshodi, Ojuelegba, Costain da Tsibirin Legas, inda jami’an NDLEA da masu sa-kai na ECAPI suka tattauna da mazauna yankuna, matasa, da kuma wadanda ake zargi da amfani da kwayoyi, ta amfani da harsunan gida daban-daban,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

Ya kuma bayyana shirye-shiryen fadada gangamin yaki da kwayoyi zuwa dukkan jihohi 36 na kasar nan da Babban Birnin Tarayya (FCT), inda ya kara da cewa ECAPI za ta ci gaba da aiki tare da hukumomin tsaro domin tabbatar da ci gaba da wannan yunkuri.

Adams ya bayyana hadin gwiwar da NDLEA a matsayin mai amfani kwarai, yana mai lura da cewa an kuma mika irin wannan hadin gwiwa ga sauran hukumomin tsaro da na yaki da cin hanci da rashawa.

A cewar sanarwar, Kwamandan NDLEA na Jihar Legas, Abubakar Wali, yayin gangamin wayar da kai, ya ce hukumar na karfafa dabarun aikinta ta hanyar mayar da hankali kan kwato kudade da kadarorin da aka samu daga laifukan da suka shafi kwayoyi.

Ya jaddada cewa gidajen da ake amfani da su wajen ba wa dillalan kwayoyi mafaka ba za su kara tsira ba, yana mai cewa kwace kadarori wata hanya ce mai karfi ta hana yawaitar laifukan kwayoyi.

Wali ya kara da cewa hukumar na sake ba da muhimmanci ga rigakafi da sauya tunanin al’umma, yana mai bayyana gangamin wayar da kai a tituna a matsayin muhimmin bangare na yaki da kwayoyi.

“Yakinmu bai tsaya kawai akan kama mutane da gurfanar da su a kotu ba. Yanzu muna kai hari kai tsaye ga kadarori. A Legas, mun kwace kudade, otal-otal, gidaje da sauran kadarori da ke da alaka da harkokin kwayoyi, mun kuma mayar da su cikin asusun gwamnati,” in ji shi.

“Wannan tafiyar wayar da kai ba ta zama alama kawai ba. Tana nuna kudurarmu ta fuskantar matsalar shan da fataucin kwayoyi kai tsaye. Kwayoyi na lalata rayuka, iyalai da makomar matasanmu,” ya kara da fada.

Masana sun sha yin kira ga ’yan al’umma da su shiga wannan yaki da shan miyagun kwayoyi, suna jaddada cewa hadin kan kowa da kowa ne kadai zai iya kawo karshen wannan annoba.

NDLEA
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Next Post
Garkuwa: TETFund, NSCDC Sun Hada Gwiwa Don Magance Tsaro A Makarantu

Garkuwa: TETFund, NSCDC Sun Hada Gwiwa Don Magance Tsaro A Makarantu

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.