ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Yi Alkawarin Kwace Kadarorin Da Ke Ba Da Mafaka Ga Dillalan Kayoyi

by Rabi'u Ali Indabawa
5 months ago
NDLEA

Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) tare da wata kungiyar farar hula mai suna Eagle Crime Awareness and Prebention Initiatibe (ECAPI) sun yi alkawarin kara kaimi wajen kwace kadarorin da ke da alaka da fataucin kwayoyi, da kuma gidajen da ake amfani da su wajen ba wa dillalan kwayoyi mafaka a fadin Jihar Legas.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da wanda ya kafa kuma shugaban ECAPI, Sam Adams, ya fitar a ranar Talata, wadda PUNCH Metro ta samu.

  • Kasar Sin Na Da Kayayyakin Tarihi Na Halittu Na Duniya Guda 15
  • Sojoji Sun Kashe Ɗan Fashi, Sun Kama Ɓarayin Shanu A Binuwe Da Nasarawa

A cewarsa, an yi wannan alkawari ne a ranar Asabar yayin wani babban gangamin wayar da kai kan yaki da kwayoyi, wanda Kwamitin Dabaru na NDLEA na Jihar Legas ya shirya tare da hadin gwiwar ECAPI, inda hukumomin suka kai gangamin wayar da kan jama’a zuwa manyan yankunan da ake fama da matsalar kwayoyi a jihar.

ADVERTISEMENT

“Kwayoyi na lalata rayuka, lafiya, mafarkai, har ma da tattalin arziki. Mun ayyana dokar rashin juriya gaba daya. Masu gidajen da suka bar a yi amfani da kadarorinsu wajen sayar da kwayoyi su sani cewa irin wadannan kadarori na iya fuskantar kwacewa.

“Gangamin tafiyar wayar da kan ya fara ne daga Maryland, ya bi ta Mushin, Oshodi, Ojuelegba, Costain da Tsibirin Legas, inda jami’an NDLEA da masu sa-kai na ECAPI suka tattauna da mazauna yankuna, matasa, da kuma wadanda ake zargi da amfani da kwayoyi, ta amfani da harsunan gida daban-daban,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

Ya kuma bayyana shirye-shiryen fadada gangamin yaki da kwayoyi zuwa dukkan jihohi 36 na kasar nan da Babban Birnin Tarayya (FCT), inda ya kara da cewa ECAPI za ta ci gaba da aiki tare da hukumomin tsaro domin tabbatar da ci gaba da wannan yunkuri.

Adams ya bayyana hadin gwiwar da NDLEA a matsayin mai amfani kwarai, yana mai lura da cewa an kuma mika irin wannan hadin gwiwa ga sauran hukumomin tsaro da na yaki da cin hanci da rashawa.

A cewar sanarwar, Kwamandan NDLEA na Jihar Legas, Abubakar Wali, yayin gangamin wayar da kai, ya ce hukumar na karfafa dabarun aikinta ta hanyar mayar da hankali kan kwato kudade da kadarorin da aka samu daga laifukan da suka shafi kwayoyi.

Ya jaddada cewa gidajen da ake amfani da su wajen ba wa dillalan kwayoyi mafaka ba za su kara tsira ba, yana mai cewa kwace kadarori wata hanya ce mai karfi ta hana yawaitar laifukan kwayoyi.

Wali ya kara da cewa hukumar na sake ba da muhimmanci ga rigakafi da sauya tunanin al’umma, yana mai bayyana gangamin wayar da kai a tituna a matsayin muhimmin bangare na yaki da kwayoyi.

“Yakinmu bai tsaya kawai akan kama mutane da gurfanar da su a kotu ba. Yanzu muna kai hari kai tsaye ga kadarori. A Legas, mun kwace kudade, otal-otal, gidaje da sauran kadarori da ke da alaka da harkokin kwayoyi, mun kuma mayar da su cikin asusun gwamnati,” in ji shi.

“Wannan tafiyar wayar da kai ba ta zama alama kawai ba. Tana nuna kudurarmu ta fuskantar matsalar shan da fataucin kwayoyi kai tsaye. Kwayoyi na lalata rayuka, iyalai da makomar matasanmu,” ya kara da fada.

Masana sun sha yin kira ga ’yan al’umma da su shiga wannan yaki da shan miyagun kwayoyi, suna jaddada cewa hadin kan kowa da kowa ne kadai zai iya kawo karshen wannan annoba.

NDLEA
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
Garkuwa: TETFund, NSCDC Sun Hada Gwiwa Don Magance Tsaro A Makarantu

Garkuwa: TETFund, NSCDC Sun Hada Gwiwa Don Magance Tsaro A Makarantu

LABARAI MASU NASABA

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.