ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Yi Alkawarin Kwace Kadarorin Da Ke Ba Da Mafaka Ga Dillalan Kayoyi

by Rabi'u Ali Indabawa
4 months ago
NDLEA

Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) tare da wata kungiyar farar hula mai suna Eagle Crime Awareness and Prebention Initiatibe (ECAPI) sun yi alkawarin kara kaimi wajen kwace kadarorin da ke da alaka da fataucin kwayoyi, da kuma gidajen da ake amfani da su wajen ba wa dillalan kwayoyi mafaka a fadin Jihar Legas.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da wanda ya kafa kuma shugaban ECAPI, Sam Adams, ya fitar a ranar Talata, wadda PUNCH Metro ta samu.

  • Kasar Sin Na Da Kayayyakin Tarihi Na Halittu Na Duniya Guda 15
  • Sojoji Sun Kashe Ɗan Fashi, Sun Kama Ɓarayin Shanu A Binuwe Da Nasarawa

A cewarsa, an yi wannan alkawari ne a ranar Asabar yayin wani babban gangamin wayar da kai kan yaki da kwayoyi, wanda Kwamitin Dabaru na NDLEA na Jihar Legas ya shirya tare da hadin gwiwar ECAPI, inda hukumomin suka kai gangamin wayar da kan jama’a zuwa manyan yankunan da ake fama da matsalar kwayoyi a jihar.

ADVERTISEMENT

“Kwayoyi na lalata rayuka, lafiya, mafarkai, har ma da tattalin arziki. Mun ayyana dokar rashin juriya gaba daya. Masu gidajen da suka bar a yi amfani da kadarorinsu wajen sayar da kwayoyi su sani cewa irin wadannan kadarori na iya fuskantar kwacewa.

“Gangamin tafiyar wayar da kan ya fara ne daga Maryland, ya bi ta Mushin, Oshodi, Ojuelegba, Costain da Tsibirin Legas, inda jami’an NDLEA da masu sa-kai na ECAPI suka tattauna da mazauna yankuna, matasa, da kuma wadanda ake zargi da amfani da kwayoyi, ta amfani da harsunan gida daban-daban,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

Ya kuma bayyana shirye-shiryen fadada gangamin yaki da kwayoyi zuwa dukkan jihohi 36 na kasar nan da Babban Birnin Tarayya (FCT), inda ya kara da cewa ECAPI za ta ci gaba da aiki tare da hukumomin tsaro domin tabbatar da ci gaba da wannan yunkuri.

Adams ya bayyana hadin gwiwar da NDLEA a matsayin mai amfani kwarai, yana mai lura da cewa an kuma mika irin wannan hadin gwiwa ga sauran hukumomin tsaro da na yaki da cin hanci da rashawa.

A cewar sanarwar, Kwamandan NDLEA na Jihar Legas, Abubakar Wali, yayin gangamin wayar da kai, ya ce hukumar na karfafa dabarun aikinta ta hanyar mayar da hankali kan kwato kudade da kadarorin da aka samu daga laifukan da suka shafi kwayoyi.

Ya jaddada cewa gidajen da ake amfani da su wajen ba wa dillalan kwayoyi mafaka ba za su kara tsira ba, yana mai cewa kwace kadarori wata hanya ce mai karfi ta hana yawaitar laifukan kwayoyi.

Wali ya kara da cewa hukumar na sake ba da muhimmanci ga rigakafi da sauya tunanin al’umma, yana mai bayyana gangamin wayar da kai a tituna a matsayin muhimmin bangare na yaki da kwayoyi.

“Yakinmu bai tsaya kawai akan kama mutane da gurfanar da su a kotu ba. Yanzu muna kai hari kai tsaye ga kadarori. A Legas, mun kwace kudade, otal-otal, gidaje da sauran kadarori da ke da alaka da harkokin kwayoyi, mun kuma mayar da su cikin asusun gwamnati,” in ji shi.

“Wannan tafiyar wayar da kai ba ta zama alama kawai ba. Tana nuna kudurarmu ta fuskantar matsalar shan da fataucin kwayoyi kai tsaye. Kwayoyi na lalata rayuka, iyalai da makomar matasanmu,” ya kara da fada.

Masana sun sha yin kira ga ’yan al’umma da su shiga wannan yaki da shan miyagun kwayoyi, suna jaddada cewa hadin kan kowa da kowa ne kadai zai iya kawo karshen wannan annoba.

NDLEA
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja
Kotu Da Ɗansanda

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

May 2, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

April 25, 2026
An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya

April 25, 2026
Next Post
Garkuwa: TETFund, NSCDC Sun Hada Gwiwa Don Magance Tsaro A Makarantu

Garkuwa: TETFund, NSCDC Sun Hada Gwiwa Don Magance Tsaro A Makarantu

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.