ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

by Bello Hamza
54 minutes ago
Arzikin

Dorewa da ingantaccen fannin Tashoshin Jiragen Ruwa na Africa ta Gabas da Afirka ta Tsakiya shi ne, babban ginshikin ci gaba wanzuwar tattalin arzikin duniya.

Shugaban Hukumar Kula da Sufurin Tashoshin Jiragen Ruwa na Kasa Dakta Abubakar Dantsoho ya yi wannan furucin.

Dantsoho ya bayyana haka ne, a jihar bayan kammala taron Daraktocin mahukuntan kungiyar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa na Africa ta Gabas da Afirka ta Tsakiya wato PMAWCA.

ADVERTISEMENT

Hukumar NPA ce, ta karbi bakuncin taron wanda ya samu halartar manyan shugabanin Hukumomin kula da Tashoshin Jiragen Ruwa da suka fito daga yankunan.

A lokacin taron, shugabanin sun tattauna kan batutuwa da dama da suka hada da, yadda za a kara inganta ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwan da ke a yankunan da samar da kayan aiki na zamani tare da ci gaba da kara karfafa hadaka da hadin kai.

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe

A yayin taron, an kuma tattauna, kan yadda za a kara karfafa tsaro a tekunan da ke a yankunan da kara bunkasa hada-hadar kasuwanci da samar da kayan aiki na zamani a Tashoshin Jiragen Ruwa da ke yankunan.

Ministan kula da bunkasa fannin tattalin arziki na Teku Gboyega Oyetola, shi ma ya halarci taron.

Dantsoho a jawabinsa a wajen taron ya bayyana cewa, Tashoshin Jiragen Ruwa har yanzu, su ne kan gaba wajen samar da damar gudanar da hada hadar-hadar kasuwancida kuma kara habaka fannin tattalin arzikin duniya.

Dantsoho, wanda kuma shi ne shugaban kungiyar ta PMAWCA ya yi nuni da cewa, daukacin shugabanin da kuma masu Ruwa da tsaki a fannin ke a yankunan akwai gudunmawar da da su taka wajen kara saita alkiblar fannin na Sufurin Jiragen Ruwa da ke a yankunan.

Ya kara da cewa, Tashoshin Jiragen Ruwa na ci gaba da Kasancewa hanyoyin da ke bayar da gagarumar gudunmawa wajen hada kasuwanin kasa da kasa, musamman wajen kara bunkasa fannin tattalin arziki.

Ya ci gaba da cewa, hakan na kara haifar da gudanar da shugabanci na gari tare da kuma cimma burin da aka sanya a gaba, a fannin.

Shugaban ya kuma kara jaddada cewa ci gaba da kara tumbatsar tattalin arzikin duniya, hade yake da irin kokarin da Tashoshin Jiragen Ruwa suke yi, musamman a yankuna maso tasowa da ake da bukatar kayan aiki, domin a kara bunkasa gasa a bangaren sufurin Jiragen Ruwa a fadin duniya.

Shugaban ya kuma bayar da tabbacin cewa, Hukumar ta NPA, ba za ta yi kasa a guiwa, wajen ci gaba da samar da kyakyawan yanayi domin a kara ciyar da yankin gaba.

An kuma tattauna kan rahoton ayyukan kwamitin tare da kuma duba ci gaban da aka samu a tsakanin Tashoshin Jiragen Ruwa da ke a yankunan.

Arzikin
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000
Tattalin Arziki

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
Tattalin Arziki

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe

May 29, 2026
Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
Tattalin Arziki

Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho

May 29, 2026

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

June 5, 2026
Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 5, 2026
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026
Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

June 5, 2026
Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.