ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

DSS Ta Cafke Wanda Ya Yi Garkuwa Gami Da Kashe Wata Farfesa A 2023

by Leadership Hausa
5 months ago

Daga Rabiu Ali Indabawa

Jami’an Hukumar Tsaron Farin kaya (DSS) sun kama wasu mutane biyu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, wadanda ake danganta su da sacewa da kashe wata farfesa a fannin ilimin jijiyoyin kwakwalwa, Ekanem Philip-Ephraim, a Jihar Cross Riber a shekarar 2023.

An sace Philip-Ephraim ne a ranar 13 ga Yulin 2023 a ofishinta da ke Calabar, Jihar Cross Riber, daga bisani kuma aka tabbatar cewa masu garkuwar sun kashe ta.

  • Batutuwan Da Suka Ci Wa ‘Yan Adawa Tuwo A Ƙwarya A Siyasar 2025
  • Sama Da Kwantainoni 600 Ke Sauka Duk Wata A Defo Din Kano —Mahukunta

A cewar tsohon Shugaban Kungiyar Likitocin Nijeriya (NMA) reshen Jihar Cross Riber, Dakta Felid Archibong, masu garkuwar sun boye kansu a matsayin marasa lafiya ne, kuma yayin da take duba su, sai suka fito da makamai suka yi awon gaba da ita da misalin karfe 7:15 na yamma.

ADVERTISEMENT

Sacewarta ta sa reshen NMA na jihar ya janye ayyukan lafiya a matsayin zanga-zanga, inda suka bukaci a ceto ta.

Jami’an DSS da suka yi magana a ranar Litinin bisa sharadin a sakaya sunansu, sun bayyana cewa an kama wadanda ake zargin wanda aka bayyana su a matsayin shugaban gungun masu laifi mai shekaru 23, Patrick Essien Etim, da kuma Bassey Antiha Asukuo mai shekaru 40 ne a ranar 27 ga Disamba a wani asibiti a jihar, yayin da ake zargin suna shirin sace wani babban likita.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi

NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano

Daya daga cikin jami’an ya ce DSS na bibiyi gungun tun daga Yulin 2023, lokacin da wasu ’yan bindiga da suka boye kansu a matsayin marasa lafiya suka sace Philip-Ephraim a asibitinta mai zaman kansa da ke hanyar Atimbo, Calabar.

“Jami’anmu, a ranar 27 ga Disamba, sun kama shugaban gungun da wani wanda ake zargi da sacewa da kashe wata fitacciyar farfesa a fannin ilimin jijiyoyin kwakwalwa, Ekanem Philip-Ephraim, a shekarar 2023.

“Shugaban gungun, Patrick Essien Etim mai shekaru 23, da abokin aikinsa, Bassey Antiha Asukuo mai shekaru 40, an cafke su a wani asibiti a Jihar Cross Riber.

“Mutanen biyu sun amsa laifin, inda suka bayyana cewa sun kashe farfesar bayan sun karbi kudaden fansa daga daya daga cikin iyalinta.”

“Shekaru biyu kenan na azaba ga ’yan uwanta da masoyanta, suna cikin rashin sanin abin da ya faru da farfesar. Ina ganin da wannan kamun, iyalinta da masoyanta za su samu nutsuwa a karshe da kuma rufewar zuciya da suka dace,” in ji majiyar.

Majiyar ta kara da cewa wadanda ake zargin sun kuma amsa sace wasu mutane tare da lalata wayoyin wutar lantarki.

Wani wanda ake zargi, mai suna Isaac Ekpeyong, shima jami’an DSS sun kama shi.

A cewar majiyar, wadannan kamun suna nuna kokarin DSS na ci gaba da tarwatsa cibiyoyin aikata laifuka da kuma kara tabbatar da tsaron al’umma.

“Wannan gagarumar nasara na nuna jajircewar DSS wajen komawa yin ayyukanta na boye da kuma dawo da tsaron jama’a a fadin kasar,” in ji majiyar.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi

June 1, 2026
NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
Tsaro

NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano

May 31, 2026
Yadda Muka Kashe Masu Garkuwa 4 Da Suke Shirin Kai Hari Kan Attajirai A Legas —CP
Tsaro

Yadda Muka Kashe Masu Garkuwa 4 Da Suke Shirin Kai Hari Kan Attajirai A Legas —CP

May 31, 2026
Next Post
Jihar Neja Ta Buɗe Makarantu Bayan Ceto Ɗaliban Da Aka Sace

Jihar Neja Ta Buɗe Makarantu Bayan Ceto Ɗaliban Da Aka Sace

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.