ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

DSS Ta Cafke Wanda Ya Yi Garkuwa Gami Da Kashe Wata Farfesa A 2023

by Leadership Hausa
6 months ago

Daga Rabiu Ali Indabawa

Jami’an Hukumar Tsaron Farin kaya (DSS) sun kama wasu mutane biyu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, wadanda ake danganta su da sacewa da kashe wata farfesa a fannin ilimin jijiyoyin kwakwalwa, Ekanem Philip-Ephraim, a Jihar Cross Riber a shekarar 2023.

An sace Philip-Ephraim ne a ranar 13 ga Yulin 2023 a ofishinta da ke Calabar, Jihar Cross Riber, daga bisani kuma aka tabbatar cewa masu garkuwar sun kashe ta.

  • Batutuwan Da Suka Ci Wa ‘Yan Adawa Tuwo A Ƙwarya A Siyasar 2025
  • Sama Da Kwantainoni 600 Ke Sauka Duk Wata A Defo Din Kano —Mahukunta

A cewar tsohon Shugaban Kungiyar Likitocin Nijeriya (NMA) reshen Jihar Cross Riber, Dakta Felid Archibong, masu garkuwar sun boye kansu a matsayin marasa lafiya ne, kuma yayin da take duba su, sai suka fito da makamai suka yi awon gaba da ita da misalin karfe 7:15 na yamma.

ADVERTISEMENT

Sacewarta ta sa reshen NMA na jihar ya janye ayyukan lafiya a matsayin zanga-zanga, inda suka bukaci a ceto ta.

Jami’an DSS da suka yi magana a ranar Litinin bisa sharadin a sakaya sunansu, sun bayyana cewa an kama wadanda ake zargin wanda aka bayyana su a matsayin shugaban gungun masu laifi mai shekaru 23, Patrick Essien Etim, da kuma Bassey Antiha Asukuo mai shekaru 40 ne a ranar 27 ga Disamba a wani asibiti a jihar, yayin da ake zargin suna shirin sace wani babban likita.

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

Daya daga cikin jami’an ya ce DSS na bibiyi gungun tun daga Yulin 2023, lokacin da wasu ’yan bindiga da suka boye kansu a matsayin marasa lafiya suka sace Philip-Ephraim a asibitinta mai zaman kansa da ke hanyar Atimbo, Calabar.

“Jami’anmu, a ranar 27 ga Disamba, sun kama shugaban gungun da wani wanda ake zargi da sacewa da kashe wata fitacciyar farfesa a fannin ilimin jijiyoyin kwakwalwa, Ekanem Philip-Ephraim, a shekarar 2023.

“Shugaban gungun, Patrick Essien Etim mai shekaru 23, da abokin aikinsa, Bassey Antiha Asukuo mai shekaru 40, an cafke su a wani asibiti a Jihar Cross Riber.

“Mutanen biyu sun amsa laifin, inda suka bayyana cewa sun kashe farfesar bayan sun karbi kudaden fansa daga daya daga cikin iyalinta.”

“Shekaru biyu kenan na azaba ga ’yan uwanta da masoyanta, suna cikin rashin sanin abin da ya faru da farfesar. Ina ganin da wannan kamun, iyalinta da masoyanta za su samu nutsuwa a karshe da kuma rufewar zuciya da suka dace,” in ji majiyar.

Majiyar ta kara da cewa wadanda ake zargin sun kuma amsa sace wasu mutane tare da lalata wayoyin wutar lantarki.

Wani wanda ake zargi, mai suna Isaac Ekpeyong, shima jami’an DSS sun kama shi.

A cewar majiyar, wadannan kamun suna nuna kokarin DSS na ci gaba da tarwatsa cibiyoyin aikata laifuka da kuma kara tabbatar da tsaron al’umma.

“Wannan gagarumar nasara na nuna jajircewar DSS wajen komawa yin ayyukanta na boye da kuma dawo da tsaron jama’a a fadin kasar,” in ji majiyar.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tsaro

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

July 11, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’
Tsaro

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Next Post
Jihar Neja Ta Buɗe Makarantu Bayan Ceto Ɗaliban Da Aka Sace

Jihar Neja Ta Buɗe Makarantu Bayan Ceto Ɗaliban Da Aka Sace

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.