Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya kwana a hannun Hukumar EFCC bayan ya amsa gayyatar da hukumar ta yi masa.
Mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Muyiwa Adekeye, ya ce El-Rufai ya je ofishin EFCC a ranar Litinin inda jami’ai suka riƙa yi masa tambayoyi, kuma ya ci gaba da kasancewa a hannunsu har ya kwana.
- Hedikwatar Tsaro Ta Tabbatar Da Isowar Sojojin Amurka A Jihar Bauchi
- Larabawan Da Suka Dauki Kasadar Ceton Yahudawa Lokacin Kisan Kiyashi
Rahotanni sun ce ana tambayarsa ne kan zargin badaƙalar a lokacin da yake gwamna daga 2015 zuwa 2023.
Har yanzu ba a san tsawon lokacin da zai ci gaba da zama a hannun hukumar ba, amma wata majiya ta ce akwai yiwuwar a kai shi kotu.
A lokaci guda, Hukumar DSS ta shigar da ƙara a kansa kan zargin yin kutse a wayar mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkar tsaro, Nuhu Ribadu.
A baya, yayin wata hira da gidan talabijin na ARISE, El-Rufai ya ce wani ne ya yi kutse awayar Ribadu ya ji lokacin da ya bayar da umarnin kama shi.















Discussion about this post