Gwamnatin Amurka ta ƙwace kadarorin wasu ‘yan Nijeriya takwas saboda zargin cewa suna taimaka wa ayyukan ta’addanci, ciki har da ƙungiyar Boko Haram da ISIL.
Hukumar kula da kadarorin ƙasashen waje ta ma’aikatar baitulmalin Amurka ta ce ana zargin mutanen da aikata laifukan kutse ta intanet da wasu hanyoyi domin tallafa wa ta’addanci.
- Nahiyar Afrika Ta Yaba Da Sakon Xi Jinping Ga Taron AU
- Fiye Da Yara Miliyan 2 Ne Ke Gararamba Da Bacci A Wuri Mai Ƙazanta A Kano – GIOPPINI
Ɗaya daga cikinsu shi ne Salih Yusuf Adamu, wanda aka taɓa ɗaure shi a Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa bayan an gano ya kafa wata gidauniya da ta tara kuɗi domin taimaka wa Boko Haram a shekarar 2022.
Sauran mutanen sun haɗa da Babestan Oluwole Ademulero, Abu Abdullah ibn Umar Al-Barnawi, Abu Musab Al-Barnawi, Khaled Al-Barnawi, Ibrahim Ali Alhassan, da Abu Bakr ibn Muhammad ibn Ali Al-Mainuki.
Yawancinsu sun fito ne daga Maiduguri a Jihar Borno.
Wannan mataki na zuwa ne a lokacin da wasu ‘yan majalisar dokokin Amurka suka ba da shawarar a ƙaƙaba takunkumi ga tsohon gwamnan Kano Rabiu Kwankwaso da kuma ƙungiyar Miyetti Allah, bisa zargin alaƙa da ta’addanci da cin zarafin Kiristoci.
A watan Oktoban 2025, shugaban Amurka Donald Trump ya sake bayyana cewa za a saka Nijeriya cikin jerin ƙasashen da ke da damuwa, yana mai zargin ana take ‘yancin addini a ƙasar.















Discussion about this post