A yau Litinin ne Nijeriya za ta san matsayinta kan fatan komawa gasar cin Kofin Duniya ta 2026, yayin da FIFA ke shirin yanke hukunci kan ƙarar da Nigeria Football Federation (NFF) ta shigar a kan Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congo, bisa zargin saka ’yan wasa shida da ba su cancanta ba a wasan share fage.
NFF ta shigar da ƙarar a ranar 15 ga Disamba, 2025, tana mai cewa sauye-sauyen dokoki sun sa wasu ’yan wasan Congo ba su cancanci buga wasan ƙarshe na neman gurbin shiga gasar ta Afirka a watan Nuwamba 2025 ba. Nijeriya ta fice daga gasar ne bayan ta sha kashi da ci 4-3 a bugun fenariti.
- Nijeriya Ta Koma Matsayi Na 26 A Jadawalin Iya Taka Leda Na Hukumar FIFA
- FIFA Za Ta Bayar Da Dala Miliyan 50 Ga Kasar Da Ta Lashe Gasar Cin Kofin Duniya
Idan FIFA ta samu Congo da laifi, akwai yiwuwar a mayar da Nijeriya cikin jerin ƙasashen da za su fafata a wasan ƙarshe na neman tikitin zuwa gasar, wanda za a buga a Mexico a watan Maris.
Sakataren NFF, Dr. Mohammed Sanusi, ya ce suna da yakini kan hujjojin da suka gabatar, kuma suna fatan hukuncin da za a yanke yau zai kasance a gare su.















Discussion about this post