Fadar Shugaban Ƙasa ta yi ba’a ga jam’iyyar NDC (Nigeria Democratic Congress) kan abin da ta bayyana a matsayin gazawar jam’iyyar wajen gabatar da cikakken kundi manufofi ko tsare-tsaren mulki ga ‘yan Nijeriya gabanin zaɓen 2027.
Mai bai wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu shawara kan yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya ce ya yi ƙoƙarin duba kundin manufofin jam’iyyar a shafinta na intanet sau biyu amma bai samu komai ba. Ya ce hakan ya sa yake tambayar ainihin alkiblar siyasar jam’iyyar da kuma ko tana da wani tsari daban da Ajandar “Renewed Hope” ta jam’iyyar APC.
A wata wallafa da ya yi a shafinsa na X, Onanuga ya ce duk lokacin da ya yi ƙoƙarin sauke kundin manufofin jam’iyyar daga shafin ta, sai tsarin ya mayar masa da sakon “No document found.” Ya ƙara da cewa, “Kamar ADC, NDC ma har yanzu ba ta da wani shiri bayyananne ga Nijeriya.”
Ya kuma ce duk da iƙirarin jagoran jam’iyyar, Seriake Dickson, cewa NDC za ta fafata da aƙida a zaɓen 2027, har yanzu jam’iyyar ba ta ɗora wani cikakken kundin manufofi a shafinta ba tun bayan rajistarta a watan Fabrairu. A cewarsa, abubuwan da aka wallafa a matsayin “ginshiƙai shida” ba su kai matsayin cikakken tsarin mulki ba.
Onanuga ya kuma caccaki Peter Obi da Rabiu Musa Kwankwaso, inda ya bayyana su a matsayin ‘yan siyasar da ke neman mafaka a jam’iyyar bayan ficewarsu daga ADC. Ya ce NDC a yanzu tana kama da “mafakar ‘yan siyasar da suka rasa matsuguni da masu neman tsira ta kowace hanya.”















Discussion about this post