Fadar Shugaban Kasa ta yi martani ga tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party a 2023, Peter Obi, bayan ficewarsa daga jam’iyyar ADC, inda ta bayyana shi a matsayin “ɗan siyasa mai yawo.”
Mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ne ya bayyana hakan a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, inda ya yi watsi da dalilan da Obi ya bayar na ficewarsa daga jam’iyyar.
Onanuga ya ce dalilan da Obi ya bayar ba su da tushe, yana mai bayyana su a matsayin maganganu marasa ma’ana. Ya kuma zargi tsohon gwamnan Anambra da yin siyasa ta amfani da dama maimakon tsayawa tsayin daka a fuskanci wahala.
Har ila yau, ya yi zargin cewa Obi na kaucewa fafatawa da manyan ‘yan siyasa irin su Atiku Abubakar da kuma Rotimi Amaechi, yana mai cewa yana zaɓar hanya mai sauƙi a siyasance.
A ƙarshe, ya ƙara da cewa Obi na yawan dora laifin matsalolin ƙasa kan gwamnati ba tare da duba kansa ba, yana mai maraba da shi zuwa fafatawar zaɓen 2027.














Discussion about this post