Sanatan da ke wakiltar Gombe ta Tsakiya, Muhammad Danjuma Goje, ya yi watsi da tsarin masalaha (consensus) da jam’iyyar APC ta amince da shi a jihar Gombe, yana mai cewa tsarin bai dace da dokokin zaɓe ba.
Hakan na zuwa ne bayan taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar da Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya jagoranta, inda aka bayyana DCP Mohammed Ahmadu Deba (mai ritaya) a matsayin ɗan takarar masala na kujerar Sanata a yankin.
A wata sanarwa da hadiminsa Barrister Saidu Muazu Kumo ya fitar, Goje wanda ke neman wa’adi na biyar a Majalisar Dattawa, ya ce taron da aka yi bai haɗa dukkan ‘yan takara masu sahihanci a jam’iyyar ba, domin a cewarsa, an taƙaita shi ne ga gwamna da wasu tsirarun ‘yan takara kawai.
Ya ƙara da cewa dokar zaɓe ta ƙasa ta tanadi hanyoyi biyu kacal na sahihiyar fitar da ‘yan takara, wanda dole ne jam’iyyu su bi su domin tabbatar da gaskiya da adalci a tsarin zaɓe. Ya jaddada cewa hanyoyin sun haɗa da gudanar da zaɓen fidda gwani kai tsaye wanda INEC da jami’an tsaro za su sa ido a kai.
Kumo ya kuma bayyana cewa akwai ‘yan takara da dama da suka sayi fom ɗin nuna sha’awa da na tsayawa takara, amma ba su halarci taron haɗakar ba, lamarin da ya sa tsarin bai zama cikakke ba. Ya ce zaɓen ɗan takara ta hanyar haɗakar ya sabawa dokokin zabe da kuma ƙa’idojin dimokuraɗiyya.
A ƙarshe, Goje ya buƙaci jam’iyyar ta gudanar da sahihin zaɓen fidda gwani domin bai wa kowa dama iri ɗaya, yana mai gargaɗin cewa duk wani tsarin da ya saɓawa doka na iya haifar da rikici a cikin jam’iyyar gabanin zaɓen 2027.















Discussion about this post