Wata ƙungiya mai zaman kanta, Global Improvement of Less Privileged Persons Initiative (GIOPPINI), ta ce sama da yara miliyan biyu ne ke kwana a muhalli mara tsaro da rashin tsafta a Kano a kullum. Daraktan zartarwa na ƙungiyar, Mohammed Ali Mashi, ya ce binciken da suka gudanar ne ya fitar da wannan ƙididdiga, yana mai bayyana lamarin a matsayin abin tayar da hankali.
A cewarsa, an gano yaran na zaune a wurare daban-daban a cikin birnin Kano, ciki har da filin sukuwa, da Central Hotel, da tashar jirgin ƙasa, da titin asibitin Nassarawa, da gadar Dangi, da Zoo Road, da gadar Lado, da Sabon Gari, da tashar Mariri da Kofar Ruwa. Ya ce da dama daga cikinsu sun fito ne daga jihohi maƙwabta ko karkara da sunan neman ilimin Alƙur’ani, amma yunwa da rashin kulawa suka sa suka bar makaranta suna rayuwar titi.
- Tinubu Ya Tura Kashim Shettima Kano, Ya Yi Alƙawarin Tallafin Kuɗi Ga Ƴan Kasuwar Singa
- Tinubu, Shettima Zasu Ziyarci Kano Halartar Tarɓar Gwamna Yusuf Zuwa APC
Mashi ya yi gargaɗin cewa idan ba a ɗauki matakin gaggawa ba, matsalar na iya rikiɗewa zuwa barazana ga tsaro da zaman lafiyar jihar, domin rayuwar titi na jefa yara cikin aikata laifi da cin zarafi. Ya ce lamarin ba na jin ƙai kaɗai ba ne, illa ma barazana ce ga zaman lafiya.
Ya buƙaci gwamnati, shugabannin al’umma da na addini da ƙungiyoyin farar hula su haɗa kai wajen samar da shirye-shiryen gyara da mayar da yaran cikin al’umma ta hanyar samar musu da mafaka, da abinci, da lafiya da ilimi. Haka kuma ya jaddada buƙatar tsare-tsaren gwamnati da za su daidaita zirga-zirgar yara tsakanin jihohi da kuma tabbatar da kulawa ga iyalai masu rauni domin daƙile ci gaba da faɗaɗar talauci da sakaci.















Discussion about this post