Wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun kai hari garin Digare a ƙaramar hukumar Alkaleri ta Jihar Bauchi, inda suka sace mutum huɗu daga iyalan Babban Limamin JIBWIS, Imam Abubakar Muhammad Digare. Harin ya faru da misalin ƙarfe 10:34 na dare a ranar Asabar, lokacin da mazauna garin ke shirin kwanciya barci, inda maharan suka riƙa harbe-harbe kafin su kutsa cikin gidan limamin.
Rahotanni sun nuna cewa maharan sun yi yunƙurin kai hari ɗakin limamin, amma ya tsere kafin su isa gare shi. Da farko sun sace matansa uku, sai dai daga bisani suka saki biyu, suka tafi da mace guda, da ɗansa da wasu yara biyu da ake zargin ’yan uwansa ne. An ce maharan sun kuma ɗauki wayar hannu da aka bari tana caji a cikin gidan.
- Sheikh Dahiru Bauchi Ya Halarci Wa’azin Da Kungiyar Izala Ta Gudanar A Bauchi
- JIBWIS Ta Aurar Da Mahaddata Da Makaranta Ƙur’ani Mata Marayu 30
Kakakin rundunar ’yansandan Jihar Bauchi, SP Nafiu Abubakar, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa an sace mata huɗu a Anguwan Madaki, Degare. Ya ce haɗin gwuiwar jami’an ’yansanda, da sojoji da masu sintiri ya kai ga ceto mutum biyu ba tare da rauni ba.
Kwamishinan ’yansandan jihar, Sani-Omolori Aliyu, ya tabbatar da cewa ana ci gaba da ƙoƙarin gano inda sauran waɗanda aka sace suke da kuma cafke waɗanda suka aikata laifin, yayin da mazauna yankin ke cikin fargaba sakamakon harin.















Discussion about this post