Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya umarci Mataimakin Shugabansa, Kashim Shettima, ya jagoranci tawagar Gwamnatin Tarayya zuwa Kano domin jajanta wa waɗanda gobarar Kasuwar Singer ta shafa tare da isar da saƙon tallafi. Gobarar, wadda ta tashi a daren Asabar har zuwa safiyar Lahadi, ta lalata kayayyaki da darajarsu ta kai biliyoyin naira, kuma ita ce ta biyu cikin makonni biyu a kasuwar.
A wata sanarwa da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai, Bayo Onanuga, ya fitar, an ce tawagar za ta tashi daga Abuja a ranar Litinin. Za ta isar da ta’aziyyar shugaban ƙasa ga ’yan kasuwar tare da yin alƙawarin tallafin kuɗi domin sauƙaƙa musu radadin asara da kuma taimaka wa Jihar Kano wajen sake gaggauta buɗe kasuwar.
- Ƴan Kasuwa 7 Sun ɓace, Asarar Dukiya Ta Haura Biliyan 5 A Gobarar Kasuwar Singa
- Gobara Ta Sake Tashi A Kasuwar Singa A Kano
Mambobin tawagar sun haɗa da Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas; da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin; da Sanata Kawu Ismaila; da Hon. Abubakar Kabir Bichi, Shugaban Kwamitin Kasafin Kuɗi na Majalisar Wakilai. Haka kuma, Ministan Jin-ƙai da Agajin Gaggawa, Dr. Bernard M. Doro, da Darakta-Janar na Hukumar bayar da tallafin gaggawa (NEMA), Zubaida Umar, na cikin tawagar.
Sanarwar ta ce Tinubu ya riga ya tattauna ta wayar tarho da Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, inda ya nuna alhini kan lamarin. Ya kuma umarci a gudanar da cikakken bincike kan musabbabin maimaituwar gobarar kasuwanni domin daƙile aukuwar irin wannan a nan gaba.















Discussion about this post