ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gidauniyar Dangote Da Gwamnatin Kano Za Su Yi Yaki Da Cutar Tamowa

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Tamowa

Gidauniyar Aliko Dangote da hadin guiwar Gwamnatin jihar Kano, asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) tare da kuma gidauniyar Bill and Melinda Gates sun rabba hannun yarjejeniyar fahimtar juna domin yin aiki tare wajen yaki da cutar Tamowa da yara ke fama da shi sakamakon karancin samun abinci mai gina jiki a jihar Kano.

Baya ga bangaren kula da cutar Tamowar, bangarorin za kuma su taimaka wajen inganta kiwon lafiya a jihar tare da kula da yin rigakafi a kai a kai domin kyautata kiwon lafiya musamman na yara da mata.

  • Manoma Sun Koka Kan Hauhawar Farashin Takin Zamani

Jimkadan bayan rabbata hannun a ranar Laraba da ya gudana a fadar Gwamnatin jihar Kano, babban darakta mai cikakken iko na gidauniyar Dangote, Zouera Yousefou, ta taya Gwamnatin jihar Kano murnar kawowa wannan matakin da kuma irin nasarorin da aka samu tun lokacin da suka fara sanya hannun yarjejeniya na farko a 2013 da na biyu a 2017 har zuwa yanzu da suka sake sanya hannu a mataki na uku.

ADVERTISEMENT

Misis Yousefou ta kuma jinjina wa Gwamnatin Kano din bisa ririta kudaden da aka ware na rigakafi kan hakan ya ce jihar ta samu karin kaso domin kara mata azama kan wannan fannin.

MD/CEO ta kuma kara da cewa bangarorin abokan jeren sun samu nasarori sosai wajen rage kaifin mace-macen mata masu juna biyu da yara a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

Ta ce jami’ansu na sanya ido domin ganin ana tafiyar da lamura yadda suka kamata. Ta nemi sarakunan gargajiya da su kara himma wajen fadakar da al’ummar su muhimmancin kiwon lafiya da amsar rigakafi, abinci mai gina jiki, kula da mata masu juna biyu da sauran bangarorin lafiya.

Ta bada tabbacin gidauniyar nasu na cigaba da taimakawa a fannin kiwon lafiya musamman na yara da mata.

A nashi jawabin, gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya ce jihar ta samu nasarori masu tarin yawa a bangaren kula da lafiyar al’umma.

A cewarsa, gwamnatinsa ba ta wasa sako-sako da harkar kiwon lafiya a kowani lokaci ta hanyar inganta kanana da manyan asibitin kula da lafiya tare da samar da wadatatun ma’aikatan da za su kula da su.

Ganduje ya ce hatta sanya hannun yarjejeniyar na nuni da himmatuwar Gwamnatin ne a bangaren kiwon lafiya.

Ya tabbatar da cewa jihar da ta kula da tallafin da ta samu daga abokan jere domin cimma manufofin da aka sanya a gaba. Sai ya gode musu bisa hakan tare da basu tabbacin kokarin gwamanti a kan hakan.

Tun da farko daraktan gidauniyar Bill and Melinda Gates a Nijeriya, Jeremie Zoungrana, ya nuna farin cikinsa bisa shaida sanya hannun da suka yi

Tamowa
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
An Kashe ‘Yan Boko Haram 49 A Sansaninsu 3 Yayin Luguden Wuta Ta Sama

An Kashe 'Yan Boko Haram 49 A Sansaninsu 3 Yayin Luguden Wuta Ta Sama

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.