ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gidauniyar Dangote Da Gwamnatin Kano Za Su Yi Yaki Da Cutar Tamowa

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Tamowa

Gidauniyar Aliko Dangote da hadin guiwar Gwamnatin jihar Kano, asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) tare da kuma gidauniyar Bill and Melinda Gates sun rabba hannun yarjejeniyar fahimtar juna domin yin aiki tare wajen yaki da cutar Tamowa da yara ke fama da shi sakamakon karancin samun abinci mai gina jiki a jihar Kano.

Baya ga bangaren kula da cutar Tamowar, bangarorin za kuma su taimaka wajen inganta kiwon lafiya a jihar tare da kula da yin rigakafi a kai a kai domin kyautata kiwon lafiya musamman na yara da mata.

  • Manoma Sun Koka Kan Hauhawar Farashin Takin Zamani

Jimkadan bayan rabbata hannun a ranar Laraba da ya gudana a fadar Gwamnatin jihar Kano, babban darakta mai cikakken iko na gidauniyar Dangote, Zouera Yousefou, ta taya Gwamnatin jihar Kano murnar kawowa wannan matakin da kuma irin nasarorin da aka samu tun lokacin da suka fara sanya hannun yarjejeniya na farko a 2013 da na biyu a 2017 har zuwa yanzu da suka sake sanya hannu a mataki na uku.

ADVERTISEMENT

Misis Yousefou ta kuma jinjina wa Gwamnatin Kano din bisa ririta kudaden da aka ware na rigakafi kan hakan ya ce jihar ta samu karin kaso domin kara mata azama kan wannan fannin.

MD/CEO ta kuma kara da cewa bangarorin abokan jeren sun samu nasarori sosai wajen rage kaifin mace-macen mata masu juna biyu da yara a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

Ta ce jami’ansu na sanya ido domin ganin ana tafiyar da lamura yadda suka kamata. Ta nemi sarakunan gargajiya da su kara himma wajen fadakar da al’ummar su muhimmancin kiwon lafiya da amsar rigakafi, abinci mai gina jiki, kula da mata masu juna biyu da sauran bangarorin lafiya.

Ta bada tabbacin gidauniyar nasu na cigaba da taimakawa a fannin kiwon lafiya musamman na yara da mata.

A nashi jawabin, gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya ce jihar ta samu nasarori masu tarin yawa a bangaren kula da lafiyar al’umma.

A cewarsa, gwamnatinsa ba ta wasa sako-sako da harkar kiwon lafiya a kowani lokaci ta hanyar inganta kanana da manyan asibitin kula da lafiya tare da samar da wadatatun ma’aikatan da za su kula da su.

Ganduje ya ce hatta sanya hannun yarjejeniyar na nuni da himmatuwar Gwamnatin ne a bangaren kiwon lafiya.

Ya tabbatar da cewa jihar da ta kula da tallafin da ta samu daga abokan jere domin cimma manufofin da aka sanya a gaba. Sai ya gode musu bisa hakan tare da basu tabbacin kokarin gwamanti a kan hakan.

Tun da farko daraktan gidauniyar Bill and Melinda Gates a Nijeriya, Jeremie Zoungrana, ya nuna farin cikinsa bisa shaida sanya hannun da suka yi

Tamowa
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Umarnin Kawo Karshen Matsalar Tsaro
Rahotonni

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

September 5, 2026
Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
Rahotonni

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

September 5, 2026
Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
Rahotonni

Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki

September 5, 2026
Next Post
An Kashe ‘Yan Boko Haram 49 A Sansaninsu 3 Yayin Luguden Wuta Ta Sama

An Kashe 'Yan Boko Haram 49 A Sansaninsu 3 Yayin Luguden Wuta Ta Sama

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.