Sabon Mashawarcin Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT) kan bin taswirar birni ta ainihi, Muktar Galadima (Wazirin Katsina Ala), ya bayyana aniyarsa ta amfani da gogewa da ƙwarewarsa domin tallafa wa Minista Nyesom Wike wajen dawo da Abuja kan tsari da martabar da aka gina ta a kai tun asali.
Wazirin Katsina Ala ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da manema labarai a birnin Abuja, inda ya yi tsokaci kan sabon muƙamin da Ministan Abuja ya ba shi a ranar 3 ga Disamba, 2025, jim kaɗan bayan ritayarsa daga aikin gwamnati.
- Ɗalibi A Fannin Karatun Lauya Ya Kashe Kansa A Adamawa
- Rikicin PDP Na Kara Ta’azzara, Yayin Da Bangaren Wike Ke Shirin Gudanar Da Babban Taro
Muktar Galadima (Wazirin Katsina Ala) ya shafe kusan shekaru takwas yana aiki a matsayin Daraktan Kula da Bin Tsarin Birnin Abuja wato (FCT Development Control) a bisa ƙwarewa da hikima da riƙon amana.
A cewarsa, ɗaya daga cikin manyan matakan da za a bi nan ba da jimawa ba shi ne farfaɗo da Kotun Hukunta Masu Bijirewa Dokokin Birnin Abuja, domin tabbatar da adalci da hana take-tsari da karya doka.
Haka kuma, ya bayyana shirin ƙara wayar da kan mazauna birnin, domin su fahimci cewa bin doka da tsari shi ne ginshikin ci gaba mai ɗorewa ba don a muzgunawa wani ba.
Mashawarcin ya ƙara da cewa zai yi iya ƙoƙarinsa wajen ƙarfafa manufofin Minista Wike na ganin Abuja ta zama birni abin koyi a Afirka da ma duniya baki ɗaya, duba da matsayin Najeriya ta jagora a nahiyar Afirka.
A ƙarshe, Wazirin Katsina Ala ya bayyana cewa a tsawon aikinsa ya samu nasarori masu yawa, duk da fuskantar ƙalubale iri-iri, musamman a ƙarshen aikinsa inda aka samu wasu rashin fahimta da Rundunar Sojin Ruwa ta Najeriya. Sai dai ya jaddada cewa waɗannan ƙalubale sun ƙara masa ƙwarewa da fahimtar aiki a matakin ƙasa.














