ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Laifi Tudu Ne, Lamarin Epstein Ya Tona Asirin Kasashen Yammaci Game Da Kare Hakkin Dan Adam

by Sulaiman and CGTN Hausa
5 months ago
epstein

Gawurtaccen mai lalata kananan ‘yan matan nan, Jeffrey Epstein da aka bayyana cewa ya kashe kansa lokacin da yake tsare a kurkuku, sunansa ya karade kafafen yada labaru na duniya, sabo da kaurin sunan da ya yi wajen aikata laifin safarar kananan ‘yan mata tare da rarraba su ga manyan mutane ana yi musu fyade. 

Mutuwar Jeffrey Epstein dai ta bar baya da kura, sabo da tonon sililin da ya bankado na abin kunya kan wasu fitattun mutane na duniya.

  • Ganduje Ya Musanta Zargin Nasir El-Rufai Kan Ɓacewar Dadiyata
  • Abin Da Ya Sa Manoman Rani Na Alkama Suka Samu Matsala A Kano

Asirin Epstein, ya fara tonuwa ne tun shekarar 2008, lokacin da wata kotu a birnin Florida na kasar Amurka ta samu Ba’Ameriken da laifin safarar ‘yan matan masu kananan shekaru tare da tursasa masu yin karuwanci, aka kuma yanke mashi hukuncin daurin watanni 18. Sai kuma a shekara ta 2019 gwamnati ta shigar da kararsa tare da tuhumarsa da laifin lalata da kananan ‘yan mata. To sai dai lokacin da yake tsare an wayi gari aka same shi ya kashe kansa.

ADVERTISEMENT

Mutuwar Jeffrey Epstein ta sanya allura ta tono garma sakamakon manyan mutanen da aka bankado suna da ma’amala ta kut da kut da Epstein a cikin wannan harka ta baɗala da kananan ‘yan mata. Irin wadannan mutane sun haɗa da jiga-jigan ‘yan siyasa da manyan attajirai da fitattun shugabanni na duniya.

Abin tashin hankalin a nan shi ne yadda kundin da aka fitar na baya bayan nan game da abin kunyar da aka fitar yake dauke da sunayen wasu fitattun mutane a fannin siyasa da harkar kudade daga Amerika da Turai. Irin wadannan mutane sun haɗa da shugabanni, ‘ya’yan gidan sarauta, jami’an diplomasiyya, ‘yan siyasa, masana, da masu kamfanonin jarida, an kuwa same su da alaka ta kut da kut da Mr. Epstein. Don haka yanzu kallo ya koma sama, shaho ya dauki giwa. Yanzu ba ma ta batun Epstein ake ba, yanzu hankali ya karkata kan irin wadannan manyan mutane, wadanda da bazarsu Epstein yake taka rawa.

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Yanayin mutuwar Jeffrey Epstein dai ta sanya jama’a tababa kan hakikanin ikirarin cewa kashe kansa ya yi. Fallasa sunayen irin wadannan mutane dake da alaka da Epstein ya kara jefa shakku kan yanayin mutuwar Mr. Epstein da cewa akwai rufa rufa.

Abin da mummunan lamarin na Epstein ya fallasa bai tsaya ga abin kunya ba kadai, lamarin ya nuna irin yadda ake yi wa doka karan tsaye tare da wulakantar da mutuncin dan adam a Amerika da kasashen yammaci. Wannan ya nuna ikirarin cewa kowa daidai yake da kowa a gaban shari’a a matsayin almara. Akwai shafaffu da mai wadanda doka ba ta hawa kansu, wato za su karya doka su kwana lafiya. An wayi gari a yau irin tabargazar da ake tafkawa a gwamnatin Amerika da majalisar dokokin kasar ya zubar da mutunci da kimar gwamnati a idon ‘yan kasar, musamman kan irin yadda ‘yan siyasa suka gurbace.

Wannan abin kunya da lamarin Epstein ya fallasa ya sanya tilas kasashen yammaci sun sunkuyar da kansu cikin kunya, sabo da irin babatunsu kan batun kare hakkin dan adam. Tun da ga shi yanzu ta tabbata sun gaza ba da kariya ga mutuncin kananan ‘yan matan da ake ci ma zarafi. (Lawal Mamuda)

epstein
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
epstein
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
Hakimin Da Aka Sace A Jihar Kogi Ya Shaki Iskar ‘Yanci

Kogi Ta Rufe Kasuwanni Da Filayen Motoci Don Fitar Da ‘Yan Ta’adda

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.