Gawurtaccen mai lalata kananan ‘yan matan nan, Jeffrey Epstein da aka bayyana cewa ya kashe kansa lokacin da yake tsare a kurkuku, sunansa ya karade kafafen yada labaru na duniya, sabo da kaurin sunan da ya yi wajen aikata laifin safarar kananan ‘yan mata tare da rarraba su ga manyan mutane ana yi musu fyade.
Mutuwar Jeffrey Epstein dai ta bar baya da kura, sabo da tonon sililin da ya bankado na abin kunya kan wasu fitattun mutane na duniya.
- Ganduje Ya Musanta Zargin Nasir El-Rufai Kan Ɓacewar Dadiyata
- Abin Da Ya Sa Manoman Rani Na Alkama Suka Samu Matsala A Kano
Asirin Epstein, ya fara tonuwa ne tun shekarar 2008, lokacin da wata kotu a birnin Florida na kasar Amurka ta samu Ba’Ameriken da laifin safarar ‘yan matan masu kananan shekaru tare da tursasa masu yin karuwanci, aka kuma yanke mashi hukuncin daurin watanni 18. Sai kuma a shekara ta 2019 gwamnati ta shigar da kararsa tare da tuhumarsa da laifin lalata da kananan ‘yan mata. To sai dai lokacin da yake tsare an wayi gari aka same shi ya kashe kansa.
Mutuwar Jeffrey Epstein ta sanya allura ta tono garma sakamakon manyan mutanen da aka bankado suna da ma’amala ta kut da kut da Epstein a cikin wannan harka ta baɗala da kananan ‘yan mata. Irin wadannan mutane sun haɗa da jiga-jigan ‘yan siyasa da manyan attajirai da fitattun shugabanni na duniya.
Abin tashin hankalin a nan shi ne yadda kundin da aka fitar na baya bayan nan game da abin kunyar da aka fitar yake dauke da sunayen wasu fitattun mutane a fannin siyasa da harkar kudade daga Amerika da Turai. Irin wadannan mutane sun haɗa da shugabanni, ‘ya’yan gidan sarauta, jami’an diplomasiyya, ‘yan siyasa, masana, da masu kamfanonin jarida, an kuwa same su da alaka ta kut da kut da Mr. Epstein. Don haka yanzu kallo ya koma sama, shaho ya dauki giwa. Yanzu ba ma ta batun Epstein ake ba, yanzu hankali ya karkata kan irin wadannan manyan mutane, wadanda da bazarsu Epstein yake taka rawa.
Yanayin mutuwar Jeffrey Epstein dai ta sanya jama’a tababa kan hakikanin ikirarin cewa kashe kansa ya yi. Fallasa sunayen irin wadannan mutane dake da alaka da Epstein ya kara jefa shakku kan yanayin mutuwar Mr. Epstein da cewa akwai rufa rufa.
Abin da mummunan lamarin na Epstein ya fallasa bai tsaya ga abin kunya ba kadai, lamarin ya nuna irin yadda ake yi wa doka karan tsaye tare da wulakantar da mutuncin dan adam a Amerika da kasashen yammaci. Wannan ya nuna ikirarin cewa kowa daidai yake da kowa a gaban shari’a a matsayin almara. Akwai shafaffu da mai wadanda doka ba ta hawa kansu, wato za su karya doka su kwana lafiya. An wayi gari a yau irin tabargazar da ake tafkawa a gwamnatin Amerika da majalisar dokokin kasar ya zubar da mutunci da kimar gwamnati a idon ‘yan kasar, musamman kan irin yadda ‘yan siyasa suka gurbace.
Wannan abin kunya da lamarin Epstein ya fallasa ya sanya tilas kasashen yammaci sun sunkuyar da kansu cikin kunya, sabo da irin babatunsu kan batun kare hakkin dan adam. Tun da ga shi yanzu ta tabbata sun gaza ba da kariya ga mutuncin kananan ‘yan matan da ake ci ma zarafi. (Lawal Mamuda)















Discussion about this post