ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Laifi Tudu Ne, Lamarin Epstein Ya Tona Asirin Kasashen Yammaci Game Da Kare Hakkin Dan Adam

by Sulaiman and CGTN Hausa
4 months ago
epstein

Gawurtaccen mai lalata kananan ‘yan matan nan, Jeffrey Epstein da aka bayyana cewa ya kashe kansa lokacin da yake tsare a kurkuku, sunansa ya karade kafafen yada labaru na duniya, sabo da kaurin sunan da ya yi wajen aikata laifin safarar kananan ‘yan mata tare da rarraba su ga manyan mutane ana yi musu fyade. 

Mutuwar Jeffrey Epstein dai ta bar baya da kura, sabo da tonon sililin da ya bankado na abin kunya kan wasu fitattun mutane na duniya.

  • Ganduje Ya Musanta Zargin Nasir El-Rufai Kan Ɓacewar Dadiyata
  • Abin Da Ya Sa Manoman Rani Na Alkama Suka Samu Matsala A Kano

Asirin Epstein, ya fara tonuwa ne tun shekarar 2008, lokacin da wata kotu a birnin Florida na kasar Amurka ta samu Ba’Ameriken da laifin safarar ‘yan matan masu kananan shekaru tare da tursasa masu yin karuwanci, aka kuma yanke mashi hukuncin daurin watanni 18. Sai kuma a shekara ta 2019 gwamnati ta shigar da kararsa tare da tuhumarsa da laifin lalata da kananan ‘yan mata. To sai dai lokacin da yake tsare an wayi gari aka same shi ya kashe kansa.

ADVERTISEMENT

Mutuwar Jeffrey Epstein ta sanya allura ta tono garma sakamakon manyan mutanen da aka bankado suna da ma’amala ta kut da kut da Epstein a cikin wannan harka ta baɗala da kananan ‘yan mata. Irin wadannan mutane sun haɗa da jiga-jigan ‘yan siyasa da manyan attajirai da fitattun shugabanni na duniya.

Abin tashin hankalin a nan shi ne yadda kundin da aka fitar na baya bayan nan game da abin kunyar da aka fitar yake dauke da sunayen wasu fitattun mutane a fannin siyasa da harkar kudade daga Amerika da Turai. Irin wadannan mutane sun haɗa da shugabanni, ‘ya’yan gidan sarauta, jami’an diplomasiyya, ‘yan siyasa, masana, da masu kamfanonin jarida, an kuwa same su da alaka ta kut da kut da Mr. Epstein. Don haka yanzu kallo ya koma sama, shaho ya dauki giwa. Yanzu ba ma ta batun Epstein ake ba, yanzu hankali ya karkata kan irin wadannan manyan mutane, wadanda da bazarsu Epstein yake taka rawa.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

Yanayin mutuwar Jeffrey Epstein dai ta sanya jama’a tababa kan hakikanin ikirarin cewa kashe kansa ya yi. Fallasa sunayen irin wadannan mutane dake da alaka da Epstein ya kara jefa shakku kan yanayin mutuwar Mr. Epstein da cewa akwai rufa rufa.

Abin da mummunan lamarin na Epstein ya fallasa bai tsaya ga abin kunya ba kadai, lamarin ya nuna irin yadda ake yi wa doka karan tsaye tare da wulakantar da mutuncin dan adam a Amerika da kasashen yammaci. Wannan ya nuna ikirarin cewa kowa daidai yake da kowa a gaban shari’a a matsayin almara. Akwai shafaffu da mai wadanda doka ba ta hawa kansu, wato za su karya doka su kwana lafiya. An wayi gari a yau irin tabargazar da ake tafkawa a gwamnatin Amerika da majalisar dokokin kasar ya zubar da mutunci da kimar gwamnati a idon ‘yan kasar, musamman kan irin yadda ‘yan siyasa suka gurbace.

Wannan abin kunya da lamarin Epstein ya fallasa ya sanya tilas kasashen yammaci sun sunkuyar da kansu cikin kunya, sabo da irin babatunsu kan batun kare hakkin dan adam. Tun da ga shi yanzu ta tabbata sun gaza ba da kariya ga mutuncin kananan ‘yan matan da ake ci ma zarafi. (Lawal Mamuda)

epstein
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Sulaiman
    Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin
  • Sulaiman
    Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci
  • Sulaiman
    Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire
epstein
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

MASU ALAKA

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata
Ra'ayi Riga

Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata

June 17, 2026
Next Post
Hakimin Da Aka Sace A Jihar Kogi Ya Shaki Iskar ‘Yanci

Kogi Ta Rufe Kasuwanni Da Filayen Motoci Don Fitar Da ‘Yan Ta’adda

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Wasa 23 Da Eric Chelle Ya Gayyata Domin Buga Wasannin Sada Zumunci 

Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba

June 20, 2026
Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

June 20, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci

June 20, 2026
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

June 20, 2026
Nijeriya

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

June 20, 2026
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

June 20, 2026
A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.