Jama’a barkanmu da juma’a, barkanmu da sake kasancewa tare da wannan shafi na GORON JUMA’A. Shafin dake bawa kowa damar miƙa saƙon gaishe-gaishensa zuwa ga ƴan’uwa da abokan arziƙi, na kusa da na nesa, har ma da waɗanda aka daɗe ba a haɗu ba.
Kamar kowane mako yau ma shafin na tafe da wasu saƙonnin gaishe-gaishen da kuka aiko mana kamar haka; Gaisuwa ta musamman ga Babban Editanmu Alhaji Bello Hamza da sauran abokan aikinsa.
- Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
- Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
- Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
- Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya
- ’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa
Saƙo daga Kabeer Ilyasu, Jihar Katsina:
Ina gaida Mahaifana su ne farko, sannan ƙannena da ƴan uwa na kamar su Zahraddeen, Auwal, Aliyu, Sabeer, da Aisha da fatan sun yi juma’a lafiya.
Saƙo daga Maryama Suraj, Jihar Sokoto:
Saƙon Goron juma’a zuwa ga Sadeeƙ da Salimat Kk, da Yaya Abbas, yaya Hashim, Yaya Fu’ad. Ina gaida Ƙawar tsokanata Mummy da ƙanwarta Ummi, da wata ƙawar tawa Zainabu Abu me tagwayen suna, sai Zuhra yarinya me kyau da fatan sun yi juma’a lafiya. Sannan ina gaida Malamina Malam Hassan Sa’eed da ƙanwarsa Amina Sa’eed da fatan su ma sun yi juma’a lafiya.
Saƙo daga Nura Ahmad (Na kowa), Jihar Kaduna:
Ina gaida Jibson ɗan small, ina gaida Tahir Jarumin Maza, Ina gaida Shehi ɗan gaske, da mahaifiyata da mahaifina da ƙannena da sauran yayyena da kowa na gidanmu ina gaishe su, ina kuma gaida abokaina na layinmu baki daya dana makaranta da fatan sun yi juma’a lafiya.
Saƙo daga Fatiyya Jibril Isah, Jihar Kaduna:
Ina gaida Uwar ɗakina kuma Uwata a gurin Sana’a wato Hajiyya Aisha Mai abinci. Sannan ƙawata kuma aminiyata wato Shamsiyya, sai ƴan’uwana na gida kamar su Hajja Uwani mai Alala, sai Mardiyya, Zulai da dai sauransu. Sai ƴan’uwana dake Kano da Maiduguri da fatan sun yi sallar juma’a lafiya.
Sunana Fatima Mustapha Hashim, daga Jihar Zamfara:
Ina gaida Mamana da Baffana, sai yayata dake garin Maiduguri wato Yaya Hajiya, sai Yaya Mu’azu dayake karatu a Katsina. Sai ƙawayena na makaranta Suwaibah Muhammad, Hajara, Zauwariyya, Zaina Abdulmajeed, Rukayya Abdullahi, Kausar Nuhu, Fatima Suleiman, Aisha Hafizu, da dai sauransu. Da fatan sun yi juma’a lafiyya, Amin.
Saƙo daga Maimunatu Aliyu, Minjibir, Jihar Kano:
Ina gaida Mahaifiyata da Mahaifina, Hajiya Saratu da Alhaji Aliyu Minjibir. Sai Gidana Alhaji Musa Yusuf, sai aminiyata Hajiya Kubra Bashir Abdullahi, sai ‘Yata Mariya, da ƙannena Rashida Aliyu Minjibir, Zainab Aliyu Minjibir, Aliya Aliyu Minjibir, Aliyu Aliyu, Abubakar Aliyu Minjibir Muhammad Aliyu Minjibir, da fatan sun yi juma’a lafiya.















Discussion about this post