Jama’a barkanmu da juma’a, barkanmu da sake kasancewa tare da wannan shafi na GORON JUMA’A. Shafin dake bawa kowa damar miƙa saƙon gaishe-gaishensa zuwa ga ƴan’uwa da abokan arziƙi, na kusa da na nesa, har ma da waɗanda aka daɗe ba a haɗu ba.
Kamar kowane mako yau ma shafin na tafe da wasu saƙonnin gaishe-gaishen da kuka aiko mana kamar haka; Gaisuwa ta musamman ga Babban Editanmu Alhaji Bello Hamza da sauran abokan aikinsa.
- Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
- An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
- Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
- Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
- Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Saƙo daga Kabeer Ilyasu, Jihar Katsina:
Ina gaida Mahaifana su ne farko, sannan ƙannena da ƴan uwa na kamar su Zahraddeen, Auwal, Aliyu, Sabeer, da Aisha da fatan sun yi juma’a lafiya.
Saƙo daga Maryama Suraj, Jihar Sokoto:
Saƙon Goron juma’a zuwa ga Sadeeƙ da Salimat Kk, da Yaya Abbas, yaya Hashim, Yaya Fu’ad. Ina gaida Ƙawar tsokanata Mummy da ƙanwarta Ummi, da wata ƙawar tawa Zainabu Abu me tagwayen suna, sai Zuhra yarinya me kyau da fatan sun yi juma’a lafiya. Sannan ina gaida Malamina Malam Hassan Sa’eed da ƙanwarsa Amina Sa’eed da fatan su ma sun yi juma’a lafiya.
Saƙo daga Nura Ahmad (Na kowa), Jihar Kaduna:
Ina gaida Jibson ɗan small, ina gaida Tahir Jarumin Maza, Ina gaida Shehi ɗan gaske, da mahaifiyata da mahaifina da ƙannena da sauran yayyena da kowa na gidanmu ina gaishe su, ina kuma gaida abokaina na layinmu baki daya dana makaranta da fatan sun yi juma’a lafiya.
Saƙo daga Fatiyya Jibril Isah, Jihar Kaduna:
Ina gaida Uwar ɗakina kuma Uwata a gurin Sana’a wato Hajiyya Aisha Mai abinci. Sannan ƙawata kuma aminiyata wato Shamsiyya, sai ƴan’uwana na gida kamar su Hajja Uwani mai Alala, sai Mardiyya, Zulai da dai sauransu. Sai ƴan’uwana dake Kano da Maiduguri da fatan sun yi sallar juma’a lafiya.
Sunana Fatima Mustapha Hashim, daga Jihar Zamfara:
Ina gaida Mamana da Baffana, sai yayata dake garin Maiduguri wato Yaya Hajiya, sai Yaya Mu’azu dayake karatu a Katsina. Sai ƙawayena na makaranta Suwaibah Muhammad, Hajara, Zauwariyya, Zaina Abdulmajeed, Rukayya Abdullahi, Kausar Nuhu, Fatima Suleiman, Aisha Hafizu, da dai sauransu. Da fatan sun yi juma’a lafiyya, Amin.
Saƙo daga Maimunatu Aliyu, Minjibir, Jihar Kano:
Ina gaida Mahaifiyata da Mahaifina, Hajiya Saratu da Alhaji Aliyu Minjibir. Sai Gidana Alhaji Musa Yusuf, sai aminiyata Hajiya Kubra Bashir Abdullahi, sai ‘Yata Mariya, da ƙannena Rashida Aliyu Minjibir, Zainab Aliyu Minjibir, Aliya Aliyu Minjibir, Aliyu Aliyu, Abubakar Aliyu Minjibir Muhammad Aliyu Minjibir, da fatan sun yi juma’a lafiya.














