Wata Kotu a jihar Kaduna ta yankewa wasu tsofaffin ma’aikatan Access Bank Plc biyu hukuncin ɗaurin shekaru bakwai kan laifin sata bayan gurfanar da su da EFCC ta yi.
Waɗanda aka yankewa hukuncin sun haɗa da Obadofin Daniel Bamise da Hadiza Oyiza Yakubu. Alƙalin kotun, A.A. Bello, ya same su da laifin satar kuɗaɗe yayin da suke aiki a bankin.
Kotun ta bayyana cewa Obadofin ya saci Naira miliyan 433,000 yayin da Hadiza ta saci Naira 806,000 tsakanin watan Nuwamban 2024 zuwa Janairun 2025. Dukansu sun amsa laifin da ake tuhumarsu da shi, lamarin da ya sa lauyan masu gabatar da ƙara ya roƙi kotun ta yanke musu hukunci.
Bayan yanke hukuncin ɗaurin shekaru bakwai ga kowannensu, kotun ta ba su zaɓin biyan tara ta Naira 50,000.
Binciken EFCC ya nuna cewa mutanen biyu sun cire kuɗi ba tare da izini ba daga asusun kwastomomi 305 da suka amfana da shirin tallafin gwamnatin tarayya, inda jimillar kuɗaɗen da aka cire ta kai Naira 7,842,700.















Discussion about this post