Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Radda, ya sanya hannu kan wata dokar gaggawa da nufin daƙile yawaitar aikata laifuka, musamman daba da sara-suka a faɗin biranen jihar.
Yayin rattaba hannu kan dokar a ranar Talata, Radda ya bayyana cewa an kafa kotunan tafi-da-gidanka domin gurfanar da masu laifi cikin sauri, yana mai cewa matakin wani muhimmin ɓangare ne na ƙoƙarin gwamnati na inganta tsaro.
Gwamna Radda Ya Gargadi Ƴan NYSC Kan Shiga Ƙungiyoyin Asiri
Gwamna Radda Ya Kaddamar Da Shirin Ci Gaban Al’umma
Gwamnan ya ce tuni gwamnatin jihar ta kafa kwamitin musamman da zai magance laifuka a shekarar 2026, wanda ya haɗa da jami’an tsaro daban-daban, Hisbah da ma’aikatu masu ruwa da tsaki.
A cewarsa, kwamitin zai gano da kuma lalata hanyoyin da masu aikata laifi ke amfani da su, tare da kwace makaman da ake riƙe da su ba bisa ƙa’ida ba da kuma gurfanar da waɗanda ake zargi ta hanyar kotunan tafi-da-gidanka domin rage jinkiri a shari’a.
Radda ya jaddada muhimmancin haɗin gwuiwa da al’umma, ciki har da sarakuna da malamai, wajen tabbatar da zaman lafiya, yana mai cewa wannan mataki zai taimaka wajen rage aikata laifuka a jihar.















Discussion about this post