ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wane Ne Tunji Disu Sabon Sufeto Janar Na Ƴansanda?

by Sani Anwar
3 months ago
Tunji

An haifi Disu a Jihar Legas, a ranar 13 ga Afrilun 1966.

Disu ya yi karatun digirinsa na farko a fannin Turanci daga Jami’ar Jihar Legas (LASU), da kuma digiri na biyu a fannin harkokin gwamnati daga Jami’ar Adekunle Ajasin, Jihar Ondo.

Har ila yau, Disu ya shiga aikin Ƴansandan Nijeriya ne a ranar 18 ga Mayun 1992, inda ya fara balaguron samun ƙwarewa, wanda a yanzu ya wuce shekaru talatin.

ADVERTISEMENT

A cikin shekarun da suka gabata, ya yi ayyuka daban-daban a fannin gudanarwa, ya samu ci gaba tare da gogewa a matsayinsa na jami’in tsaro.

  • De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City
  • Yadda Muka Magance Rikicin Kabilanci Da Shaye-shayen Matasa A Masarautarmu —Sarkin Shukura

Haka zalika, ya kuma halarci kwasa-kwasai da dama a gida da waje, ciki har da samun horo ta fuskar ƙananan makamai a Botswana; horo a fannin zamba ta Intanet daga Jami’ar Cambridge da Burtaniya; Kwas a fannin Jagoranci da Dabaru a Kwalejin Ma’aikatan ƴansanda, Jos; Horo a fannin Binciken Laifuka da Nazarin Laifuka a Jami’ar Legas, da dai sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Disu dai, ya kasance tsohon kwamandan runduna ta ‘Rapid Response Sƙuad (RRS)’ a Jihar Legas, inda ya jagoranci tawagar da ta kama wasu masu aikata laifuka, musamman Ƴan damfara.

Bayan wani ɗan lokaci kaɗan, wani tsohon IGP, Usman Alkali Baba, ya naɗa shi a matsayin shugaban rundunar Ƴansanda (IRT), a ranar 2 ga watan Agustan 2021, bayan dakatar da DCP Abba Kyari.

A lokacin ya kasance mataimakin kwamishinan Ƴansanda a sashen ayyuka na hedikwatar rundunar da ke Abuja.

Disu ya kuma taɓa yin aiki a sashin binciken manyan laifuka da leƙen asiri na Jihar Ribas, a matsayin shugaba na biyu a sashin.

Daga baya kuma, ya zama kwamishinan Ƴansanda a Jihar Ribas, sannan kuma daga bisani ya koma babban birnin tarayya Abuja.

Ya kuma kasance kwamandan rundunar ƴansandan Nijeriya, reshen ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU), a yankin Darfur na ƙasar Sudan.

Kazalika, ya kasance memba na ƙungiyar shugabannin ƴansanda ta duniya, Cibiyar Hulɗa da Jama’a ta Nijeriya da Cibiyar Kula da Ma’aikata ta Chartered, da sauran ƙwararrun ƙungiyoyi.

Yayin da ya kai matsayin mataimakin Sufeto Janar, Disu ya shiga babbar rundunar ne a daidai lokacin da ƙasar nan ke fuskantar ƙalubalen tsaro da kuma ƙaruwar buƙatar yin gyara, ƙwarewa da kuma riƙon amana a cikin tsarin aikin Ƴansanda.

Naɗin Olatunji Disu a matsayin babban Sufeto Janar na Ƴansandan Nijeriya, ya ƙara jawo hankalin ɗaya daga cikin manyan kwamandojin aiki na rundunar Ƴansandan Nijeriya.

Tunji
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
El-Rufai: Baki Shi Ke Yanka Wuya

El-Rufai: Baki Shi Ke Yanka Wuya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.