An haifi Disu a Jihar Legas, a ranar 13 ga Afrilun 1966.
Disu ya yi karatun digirinsa na farko a fannin Turanci daga Jami’ar Jihar Legas (LASU), da kuma digiri na biyu a fannin harkokin gwamnati daga Jami’ar Adekunle Ajasin, Jihar Ondo.
Har ila yau, Disu ya shiga aikin Ƴansandan Nijeriya ne a ranar 18 ga Mayun 1992, inda ya fara balaguron samun ƙwarewa, wanda a yanzu ya wuce shekaru talatin.
A cikin shekarun da suka gabata, ya yi ayyuka daban-daban a fannin gudanarwa, ya samu ci gaba tare da gogewa a matsayinsa na jami’in tsaro.
- De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City
- Yadda Muka Magance Rikicin Kabilanci Da Shaye-shayen Matasa A Masarautarmu —Sarkin Shukura
Haka zalika, ya kuma halarci kwasa-kwasai da dama a gida da waje, ciki har da samun horo ta fuskar ƙananan makamai a Botswana; horo a fannin zamba ta Intanet daga Jami’ar Cambridge da Burtaniya; Kwas a fannin Jagoranci da Dabaru a Kwalejin Ma’aikatan ƴansanda, Jos; Horo a fannin Binciken Laifuka da Nazarin Laifuka a Jami’ar Legas, da dai sauransu.
Disu dai, ya kasance tsohon kwamandan runduna ta ‘Rapid Response Sƙuad (RRS)’ a Jihar Legas, inda ya jagoranci tawagar da ta kama wasu masu aikata laifuka, musamman Ƴan damfara.
Bayan wani ɗan lokaci kaɗan, wani tsohon IGP, Usman Alkali Baba, ya naɗa shi a matsayin shugaban rundunar Ƴansanda (IRT), a ranar 2 ga watan Agustan 2021, bayan dakatar da DCP Abba Kyari.
A lokacin ya kasance mataimakin kwamishinan Ƴansanda a sashen ayyuka na hedikwatar rundunar da ke Abuja.
Disu ya kuma taɓa yin aiki a sashin binciken manyan laifuka da leƙen asiri na Jihar Ribas, a matsayin shugaba na biyu a sashin.
Daga baya kuma, ya zama kwamishinan Ƴansanda a Jihar Ribas, sannan kuma daga bisani ya koma babban birnin tarayya Abuja.
Ya kuma kasance kwamandan rundunar ƴansandan Nijeriya, reshen ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU), a yankin Darfur na ƙasar Sudan.
Kazalika, ya kasance memba na ƙungiyar shugabannin ƴansanda ta duniya, Cibiyar Hulɗa da Jama’a ta Nijeriya da Cibiyar Kula da Ma’aikata ta Chartered, da sauran ƙwararrun ƙungiyoyi.
Yayin da ya kai matsayin mataimakin Sufeto Janar, Disu ya shiga babbar rundunar ne a daidai lokacin da ƙasar nan ke fuskantar ƙalubalen tsaro da kuma ƙaruwar buƙatar yin gyara, ƙwarewa da kuma riƙon amana a cikin tsarin aikin Ƴansanda.
Naɗin Olatunji Disu a matsayin babban Sufeto Janar na Ƴansandan Nijeriya, ya ƙara jawo hankalin ɗaya daga cikin manyan kwamandojin aiki na rundunar Ƴansandan Nijeriya.















Discussion about this post