ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wane Ne Tunji Disu Sabon Sufeto Janar Na Ƴansanda?

by Sani Anwar
4 months ago
Tunji

An haifi Disu a Jihar Legas, a ranar 13 ga Afrilun 1966.

Disu ya yi karatun digirinsa na farko a fannin Turanci daga Jami’ar Jihar Legas (LASU), da kuma digiri na biyu a fannin harkokin gwamnati daga Jami’ar Adekunle Ajasin, Jihar Ondo.

Har ila yau, Disu ya shiga aikin Ƴansandan Nijeriya ne a ranar 18 ga Mayun 1992, inda ya fara balaguron samun ƙwarewa, wanda a yanzu ya wuce shekaru talatin.

ADVERTISEMENT

A cikin shekarun da suka gabata, ya yi ayyuka daban-daban a fannin gudanarwa, ya samu ci gaba tare da gogewa a matsayinsa na jami’in tsaro.

  • De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City
  • Yadda Muka Magance Rikicin Kabilanci Da Shaye-shayen Matasa A Masarautarmu —Sarkin Shukura

Haka zalika, ya kuma halarci kwasa-kwasai da dama a gida da waje, ciki har da samun horo ta fuskar ƙananan makamai a Botswana; horo a fannin zamba ta Intanet daga Jami’ar Cambridge da Burtaniya; Kwas a fannin Jagoranci da Dabaru a Kwalejin Ma’aikatan ƴansanda, Jos; Horo a fannin Binciken Laifuka da Nazarin Laifuka a Jami’ar Legas, da dai sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Disu dai, ya kasance tsohon kwamandan runduna ta ‘Rapid Response Sƙuad (RRS)’ a Jihar Legas, inda ya jagoranci tawagar da ta kama wasu masu aikata laifuka, musamman Ƴan damfara.

Bayan wani ɗan lokaci kaɗan, wani tsohon IGP, Usman Alkali Baba, ya naɗa shi a matsayin shugaban rundunar Ƴansanda (IRT), a ranar 2 ga watan Agustan 2021, bayan dakatar da DCP Abba Kyari.

A lokacin ya kasance mataimakin kwamishinan Ƴansanda a sashen ayyuka na hedikwatar rundunar da ke Abuja.

Disu ya kuma taɓa yin aiki a sashin binciken manyan laifuka da leƙen asiri na Jihar Ribas, a matsayin shugaba na biyu a sashin.

Daga baya kuma, ya zama kwamishinan Ƴansanda a Jihar Ribas, sannan kuma daga bisani ya koma babban birnin tarayya Abuja.

Ya kuma kasance kwamandan rundunar ƴansandan Nijeriya, reshen ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU), a yankin Darfur na ƙasar Sudan.

Kazalika, ya kasance memba na ƙungiyar shugabannin ƴansanda ta duniya, Cibiyar Hulɗa da Jama’a ta Nijeriya da Cibiyar Kula da Ma’aikata ta Chartered, da sauran ƙwararrun ƙungiyoyi.

Yayin da ya kai matsayin mataimakin Sufeto Janar, Disu ya shiga babbar rundunar ne a daidai lokacin da ƙasar nan ke fuskantar ƙalubalen tsaro da kuma ƙaruwar buƙatar yin gyara, ƙwarewa da kuma riƙon amana a cikin tsarin aikin Ƴansanda.

Naɗin Olatunji Disu a matsayin babban Sufeto Janar na Ƴansandan Nijeriya, ya ƙara jawo hankalin ɗaya daga cikin manyan kwamandojin aiki na rundunar Ƴansandan Nijeriya.

Tunji
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Next Post
El-Rufai: Baki Shi Ke Yanka Wuya

El-Rufai: Baki Shi Ke Yanka Wuya

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.