ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wane Ne Tunji Disu Sabon Sufeto Janar Na Ƴansanda?

by Sani Anwar
5 months ago
Tunji

An haifi Disu a Jihar Legas, a ranar 13 ga Afrilun 1966.

Disu ya yi karatun digirinsa na farko a fannin Turanci daga Jami’ar Jihar Legas (LASU), da kuma digiri na biyu a fannin harkokin gwamnati daga Jami’ar Adekunle Ajasin, Jihar Ondo.

Har ila yau, Disu ya shiga aikin Ƴansandan Nijeriya ne a ranar 18 ga Mayun 1992, inda ya fara balaguron samun ƙwarewa, wanda a yanzu ya wuce shekaru talatin.

ADVERTISEMENT

A cikin shekarun da suka gabata, ya yi ayyuka daban-daban a fannin gudanarwa, ya samu ci gaba tare da gogewa a matsayinsa na jami’in tsaro.

  • De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City
  • Yadda Muka Magance Rikicin Kabilanci Da Shaye-shayen Matasa A Masarautarmu —Sarkin Shukura

Haka zalika, ya kuma halarci kwasa-kwasai da dama a gida da waje, ciki har da samun horo ta fuskar ƙananan makamai a Botswana; horo a fannin zamba ta Intanet daga Jami’ar Cambridge da Burtaniya; Kwas a fannin Jagoranci da Dabaru a Kwalejin Ma’aikatan ƴansanda, Jos; Horo a fannin Binciken Laifuka da Nazarin Laifuka a Jami’ar Legas, da dai sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Disu dai, ya kasance tsohon kwamandan runduna ta ‘Rapid Response Sƙuad (RRS)’ a Jihar Legas, inda ya jagoranci tawagar da ta kama wasu masu aikata laifuka, musamman Ƴan damfara.

Bayan wani ɗan lokaci kaɗan, wani tsohon IGP, Usman Alkali Baba, ya naɗa shi a matsayin shugaban rundunar Ƴansanda (IRT), a ranar 2 ga watan Agustan 2021, bayan dakatar da DCP Abba Kyari.

A lokacin ya kasance mataimakin kwamishinan Ƴansanda a sashen ayyuka na hedikwatar rundunar da ke Abuja.

Disu ya kuma taɓa yin aiki a sashin binciken manyan laifuka da leƙen asiri na Jihar Ribas, a matsayin shugaba na biyu a sashin.

Daga baya kuma, ya zama kwamishinan Ƴansanda a Jihar Ribas, sannan kuma daga bisani ya koma babban birnin tarayya Abuja.

Ya kuma kasance kwamandan rundunar ƴansandan Nijeriya, reshen ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU), a yankin Darfur na ƙasar Sudan.

Kazalika, ya kasance memba na ƙungiyar shugabannin ƴansanda ta duniya, Cibiyar Hulɗa da Jama’a ta Nijeriya da Cibiyar Kula da Ma’aikata ta Chartered, da sauran ƙwararrun ƙungiyoyi.

Yayin da ya kai matsayin mataimakin Sufeto Janar, Disu ya shiga babbar rundunar ne a daidai lokacin da ƙasar nan ke fuskantar ƙalubalen tsaro da kuma ƙaruwar buƙatar yin gyara, ƙwarewa da kuma riƙon amana a cikin tsarin aikin Ƴansanda.

Naɗin Olatunji Disu a matsayin babban Sufeto Janar na Ƴansandan Nijeriya, ya ƙara jawo hankalin ɗaya daga cikin manyan kwamandojin aiki na rundunar Ƴansandan Nijeriya.

Tunji
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Next Post
El-Rufai: Baki Shi Ke Yanka Wuya

El-Rufai: Baki Shi Ke Yanka Wuya

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.