Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Radda ya sayo motocin daukar marasa lafiya guda 15 domin kula da wadanda hadari ya rutsa da su a kan manyan titunan jihar.
Da yake jawabi a lokacin karbar wadannan motocin daukar marasa lafiya, shugaban ma’aikatan gidan gwamnati, Hon. Abdulkadir Mamman Nasir (ANDAJE) ya bayya cewa sayan motocin wani bangare ne na cika alkawarin da wannan gwamnatin ta yi.
- ICPC Za Ta Ci Gaba Da Binciken Tsohon Shugaban NMDPRA Duk Da Janye Ƙarar Dangote
- Harin Venezuela Ta’asa Ce Da Amurka Ke Tafkawa Tun Bayan Yakin Duniya Na Biyu
A cewarsa, wadannan motoci za su taimaka matuka gaya wajen ceto mutanen da suka samu hadari a manyan titunan da gwamnatin Jihar Katsina ta gyara da ma wadanda suke a gare.
“A daidai lokacin da ake ta kokarin ganin an kammala manyan hanyoyin da wannan gwamnatin ke yi da kuma gyaran wadanda suka lallace, lallai akwai bukatar sanya irin wadannan motoci a kan hanya ko da an samu hadari za su taimaka sosai wajen ceton rayuka,” in ji shi.
Ya kara da cewa, Gwamna Radda ya yi alkawarin cewa zai tabbatar ya samar da harkar kiwon lafiya ingantaciya a Jihar Katsina, ya ce kawo wadannan motoci shaida ce da ke tabbatar da haka.
Hon. Abdulkadir ya ba da tabbacin cewa wadannan motoci za a doro su a kan manyan hanyoyin Jihar Katsina domin su samar da kyakkyawar yanayi na kiwon lafiya, musamman wadanda suka samu hadari suna neman taimako.
Shugaban ma’aikatan fadar gwamnatin Katsina ya yi bayanin cewa gwamnan yana da wani tsari da zai kula da wadannan motoci domin dorewa da aiki da su.
Haka kuma ya ba da tabbacin cewa gwamanti za ta kafa kwamiti mai karfin gaske wanda zai hada wakilai daga hukumomin kiyaye hadura da kuma ma’aikatar lafiya ta Jihar Katsina da shugabannin kananan hukumomi domin yin aiki tare.
Ya kuma ƙara da cewa Gwamna Radda da kansa zai kaddamar da fara aikin wadannan motoci tare da rarraba su zuwa wuraren da aka tanada domin ajiye su da kuma fara aikinsu.















Discussion about this post