Gwamnatin Nijeriya ta fitar da jerin sunayen wasu mutane da ƙungiyoyi da ake zargin suna ɗaukar nauyin ayyukan ta’addanci a ƙasar.
Rahotanni sun nuna cewa jerin sunayen ya ƙunshi mutane da ƙungiyoyi da ake zargi da taimakawa ta’addanci ta hanyoyi daban-daban, ciki har da samar da kuɗi, kayan aiki, da kuma tallafi ga ƙungiyoyin ta’adda.
- Fadar Shugaban Ƙasa Ta Gargaɗi Peter Obi Kan Zargin Tinubu Na Haddasa Rikici A ADC
- Arewa Ce Za Ta Yanke Makomar Tinubu A 2027 — Primate Ayodele
Wannan mataki na daga cikin ƙoƙarin gwamnati na ƙara tsaurara yaƙi da ta’addanci, tare da katse hanyoyin samun kuɗaɗen da ke taimaka wa ayyukan ta’addanci a cikin ƙasar.
Rahoton ya ƙara da cewa hukumomin tsaro da na kuɗi sun taka muhimmiyar rawa wajen gano waɗannan sunaye, ta hanyar bincike mai zurfi da kuma sa ido kan harkokin kuɗi da ake zargin suna da alaƙa da ta’addanci.
Ana sa ran cewa wannan mataki zai taimaka wajen ƙarfafa tsaro da kuma rage ayyukan ta’addanci a Nijeriya, musamman ta hanyar hana masu ɗaukar nauyin ta’addanci damar ci gaba da ayyukansu.
Gwamnatin ta jaddada aniyarta na ci gaba da bin diddigin duk wasu da ake zargi da hannu a harkokin ta’addanci, tare da ɗaukar matakan doka a kansu.















Discussion about this post