ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tinubu Za Ta Sake Inganta NTA Da FRCN – Minista

by Sulaiman
3 years ago
Tinubu

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu ta ƙudiri aniyar aiwatar da wasu tsare-tsaren gyara da za su dawo da martabar da aka san mashahuran kafafen watsa labarai biyu ɗin nan da su, wato Hukumar Talabijin ta Nijeriya (NTA) da Hukumar Gidajen Rediyon Tarayya (FRCN).

Hadimin musamman na ministan kan harkokin yaɗa labarai, Malam Rabi’u Ibrahim, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai, cewa Ministan ya sha wannan alwashin ne a Kaduna a lokacin da ya kai ziyarar aiki a ofishin hukumomin biyu.

  • Firaministan Cuba: Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Za Ta Amfanawa Duk Duniya
  • Yadda Na Hana ‘Yan Boko Haram Mayar Da Jihar Neja Hedikwatarsu – Tsohon Gwamnan Jihar 

A yayin da ya ke magana kan babbar rawar da gidan Rediyon Tarayya na Kaduna da gidan talabijin na NTA Kaduna su ke takawa wajen jan akalar ra’ayin jama’a da watsa labarai da ɗabbaka musayar al’adu, Ministan ya ce kafafen biyu sun samu koma-baya a ‘yan shekarun nan da su ka gabata saboda watsi da su da aka yi, da rashin tarbiyyar aiki, da tsofaffin wuraren aiki da kayan aiki, wanda hakan ya karya alkadarinsu wajen yin shirye-shirye da taka muhimmiyar rawa.

ADVERTISEMENT

Ministan ya bada tabbacin cewa, gwamnatin Tinubu za ta farfaɗo da kafafen kuma ta mayar da su kan gaba a aikin rediyo da na talabijin a fadin Nijeriya.

Ya ce: “Yadda za a iya mayar da NTA da FRCN matsayin wakilan ƙwarai a tsare-tsaren Gwamnatin Tarayya sosai, tilas sai mun yi la’akari da babbar gazawarsu a yanzu a fagen da ke cike da gasa, da amfani da basira, da amfani da fasahohin zamani.

LABARAI MASU NASABA

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

“Dalilin zuwa na nan tare da Darakta-Janar na NTA da na FRCN shi ne, domin mu nemo cikakkiyar hanyar da za mu bi don magance waɗannan matsalolin, wanda ya na kan gaba cikin abubuwan da mu ka ba muhimmanci.

“Za mu duba dukkan zaɓi da ke gabanmu domin tabbatar da cewa mun dawo da martabar da NTA da FRCN su ka rasa.”

Ministan ya ce matsalar FRCN a matakin ƙasa da na jihohi ya ma fi ta’azzara, musamman ma a Rediyon Nijeriya, Kaduna, wanda ya bayyana da cewa “a shekaruj baya, sun kasance wuri ne mai daraja na yaɗa labarai wanda ya samar da zaƙaƙuran ma’aikatan rediyo.

“Hakika, Rediyo Nijeriya Kaduna na buƙatar a farfaɗo da shi da gaggawa. Babu shakka za mu ɗauki mataki da sauri a wannan aiki na ceto,” inji shi.

Idris ya ce a lokacin da ya kama aiki, ya samu kiraye-kiraye masu yawa daga sassa da dama daga masu ruwa da tsaki a kan lalacewar kafafen biyu, ya na mai nanata cewa lallai aikin da ke gabansa shi ne tabbatar da cewa an yi wa NTA da FRCN garambawul domin su cimma manufofin kafa su.

Ya ce: “Ina tabbatarwa shugabanni da ma’aikata da sauran masu ruwa da tsaki a NTA da FRCN cewa, Shugaba Tinubu ya naɗa Malam Salihu Abdulhamid Dembos da Dakta Mohammed Bulama a matsayin Darakta-Janar na NTA da FRCN ne bayan cikakken nazari kan ƙwarewarsu wajen iya kawo kyakkyawan sauyi a hukumomin biyu waɗanda babu hukumomin aikin talabijin da rediyo kamarsu wajen girma a Nijeriya da ma Afrika baki ɗaya.

“A shirye na ke in duba kowace dama da ke akwai wadda za ta bayar da duk abin da ake buƙata don tabbatar da cewa, an sama wa NTA da FRCN kayan aiki na zamani, kuma a baiwa ma’aikatansu cikakkiyar horaswa da kuma biya masu haƙƙoƙin aiki.”

Ministan ya ce ya kamata hukumomin yaɗa labaran biyu su tashi tsaye su rungumi yanayin aikin jarida wanda zamani ya kawo wajen aiki da kayan fasaha na zamani idan har su na so a yi gogayya da su, su inganta kyawun aiki, kuma sakonni su su kai ga ɗimbin masu kallo da masu saurare.

A lokacin ziyarar, Ministan da tawagarsa sun duba muhimman kayan aikin tashoshin biyu da ke cikin garin Kaduna da kuma garin Jaji a babban titin Kaduna zuwa Zariya.

Tinubu
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
  • Sulaiman
    Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • Sulaiman
    Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
  • Sulaiman
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

MASU ALAKA

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON
Labarai

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu
Labarai

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau
Rahotonni

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Next Post
Shugaba Xi Ya Yi Kira Da A Ingiza Muhimmiyar Rawa Da Tsarin Mulkin Kasa Ke Takawa A Fannin Jagorancin Kasa

Shugaba Xi Ya Yi Kira Da A Ingiza Muhimmiyar Rawa Da Tsarin Mulkin Kasa Ke Takawa A Fannin Jagorancin Kasa

LABARAI MASU NASABA

Falalar Salatut Tasbihi

Falalar Salatut Tasbihi

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.