ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gyaran Dokar Zabe: Yadda Jinkirin Majalisar Dattawa Zai Iya Kawo Tsaiko Ga Zaben 2027

by Yusuf Shuaibu
4 months ago
Zabe

Jinkirin majalisar dattawa wajen gyare-gyaren dokar zabe ta shekarar 2022, ya tsawaita lokacin shirye-shiryen hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) na fitar da jaddawalin ayyukan zaben 2027, wanda hakan zai kawo tsaiko ga zaben.

A cikin ‘yan makonnin da suka gabata, majalisar dattawa ta fuskanci suka kan jinkiri wajen gyaran dokar zabe ta shekarar 2022, wanda ka iya jefa zaben 2027 cikin rashin tabbas. An dai zargi majalisar dattawa da kawo jinkiri da gangan, wanda majalisar ta kare kanta a makon da ya gabata.

  • Rikicin Iran Da Amurka: Gabas Ta Tsakiya Ta Ɗauki Zafi
  • Yadda Fasahar Sin Ke Agaza Wa Samun Wadataccen Hatsi A Afirka

A ranar Laraba da ta wuce, yayin da aka yi tsammanin majalisar dattawa za ta karbi rahoton kwamitin kula da harkokin zabe kan dokar gyaran zabe, sai zaman majalisar ya tsaya ba zato ba tsammani. Lokacin da aka kai ga yin la’akari da takardar shafi 238, wacce aka raba wa kowane dan majalisa, an daga zaman zuwa ranar Alhamis, sakamakon rashin halartar shugaban kwamitin, Sanata Simon Lalong.

ADVERTISEMENT

“Za mu ba ‘yan majalisar dattawa damar komawa gida da rahoton su yi nazarin shi kuma idan muka dawo gobe, za mu yi wani zama na sirri na dan gajeren lokaci mu tattauna muhimman tanadi na dokar, sannan mu amince da ita,” in ji jagoran majalisar dattawa, Sanata Opeyemi Bamidele.

Duk da haka, a ranar Alhamis, majalisar dattawa ta kasa daukar wani muhimmin mataki dangane da lamarin. Tattaunawar da Bamidele ya yi alkawari bai faru ba, yayin da ba a samu wani yunkurin amincewa da dokar ba. Haka zalika, wannan ba shi ne karo na farko da aka yi irin wannan alkawarin ba kuma aka kasa cika. A watan Oktoba na shekarar 2025, Bamidele ya ce majalisar dattawa na aiki cikin sauri don guje wa bata lokaci wajen sa hannu kan amincewa da dokar zabe kafin lokacin zabe.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

“Daga yanzu (14 ga Oktoba, 2025) zuwa Disamba 2025, za mu tabbatar da kammala gyaran dokar zabe ta 2022 don ka da ta yi kusa da zaben 2027,” jagoran majalisar dattawa ya yi alkawari. Amma fiye da wata guda bayan karshen Disamba 2025, majalisar dattawa ta kasa amicewa da gyaran dokar zaben.

Sakamakon zaman na ranar Alhamis, masu ruwa da tsaki sun ci gaba da abin da aka saba gani. Majalisar dattawa tana jinkirta daukar mataki kan kudirin soke dokar zabe da gyara tun lokacin da majalisar wakilai ta amince da nata bangaren a ranar 23 ga Disamba, 2025, kafin su tafi hutu na Kirsimeti da sabuwar shekara.

A taron zaman majalisar dattawan na ranar Laraba, shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio ya shaida wa abokan aikinsa da su nazarci rahoton kwamitin kafin yin la’akari na karshe a ranar Alhamis.

“Abokan aiki masu daraja, kamar yadda jagora ya shawarce mu, don Allah mu duba rahoton sosai kafin yanke shawara na karshe gobe,” in ji shi.

Sai dai kuma a ranar Alhamis ba a sami dubawa na karshe ba. Maimakon haka, majalisar dattawa ta shiga zaman sirri na awa uku wanda ya haifar da kafa wani kwamiti na daban, wanda a zahiri ya kara daga lokacin da ake zaton amincewa kudirin a watan Fabrairu, wanda kuma shi ne watan da ake sa ran INEC za ta fitar da sanarwar zaben 2027.

Tuni dai masu ruwa da tsaki suka nuna damu cewa majalisar dattawa na yin abin da bai kamata ba, sanarwar Akpabio na kafa kwamitin wucin gadi mai mambobi bakwai ya kara ta’azzara damuwarsu. An sanya wa kwamitin, wanda ake sa ran zai bayar da rahoto ranar Talata mai zuwa, kan aiki na gyara dokar zabe.

Shugaban kwamitin, Sanata Niyi Adegbonmire, wanda shi ne shugaban kwamitin majalisar dattawa kan harkokin sahari’a, sauran mambobin kwamitin sun hada da Adamu Aliero, Aminu Tambuwal, Adams Oshiomhole, Danjuma Goje, Tony Nwoye, da Titus Zam.

Ana ana sa ran INEC za ta yi aiki da sabon dokar zabe don samar da ka’idoji na gudanar da zaben 2027, masu ruwa da tsaki na ci gaba da nuna damuwa kan takaitaccen lokaci yayin da majalisar dattawa ke jan kafa kan daukar mataki.

Sashe na 28(1) na dokar zabe ta 2022, ya umurci INEC da ta fitar da sanarwar zabe kasa da kwanaki 360 kafin ranar kada kuri’a. An yi zaben shugaban kasa na karshe a ranar 25 ga Fabrairu, 2023, tare da tsammanin cewa zaben shugaban kasa na gaba zai gudana a watan Fabrairun 2027.

Amma akwai alamun da ke nuna cewa za a iya daga babban zaben, wanda ya jefa INEC cikin rudani wajen gudanar da shiri a karamin lokaci. Tsarin gyara da ke gaban majalisar dattawa na ba da shawarar a gudanar da zaben shugaban kasa da gwamna a watan Nuwamba 2026, wanda za a gudanar da shi kusan watanni hudu kafin yadda aka tsara.

Sashe na 4(7) na kudurin gyara dokar ya bayyana cewa, “Za a gudanar da zaben shugaban kasa da gwamnonin jihohi kasa da kwanaki 185 kafin karewar wa’adin mai rike da mukamin.” Ana sa ran wa’adin masu rike da mukamai a halin yanzu zai kare a ranar 29 ga Mayu, 2027.

Idan majalisar dattawa ta amince da wannan kudirin, INEC za ta fuskanci gajeren lokaci na kammala ayyukanta. Tare da kasancewar hukumar da aka sani tana dage zabe saboda rashin isasshen shiri ko da an ba ta fiye da kwanaki 300 don yin shiri, jinkirin majalisar dattawan yana ci gaba da zama mai lahani ga gudanar da zabukan da ke tafe.

Idan majalisar dattawa ta kasa amincewa da gyaran dokar zabe a wannan makon, lokacin zai takaita sosai. Duk wani canji da aka shigar a bangaren majalisar wakilai zai bukaci a daidaita ta hanyar kwamitin kafin a amince da shi, sannan a mika wa Shugaban kasa Bola Tinubu don sanya hannu.

Wannan kalubalen ta kashe kwarin gwiwa a tsakanin masu ruwa da tsaki kan zaben 2027, wanda zai kasance sahihin zabe fiye da na 2023, wanda aka sami matsaloli na zargin rashin daidaito. Wadannan matsaloli sun karu saboda gibin da ke cikin dokar zabe ta 2022, wadda ba ta tilasta matakan bayyana gaskiya kamar isar da sakamakon zabe ta na’ura, wani mataki da zai iya rage yin magudin zabe.

Zabe
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Majalisar Ƙoli Kan Shari’ar Musulunci Ta Sake Neman A Cire Shugaban INEC

Majalisar Ƙoli Kan Shari’ar Musulunci Ta Sake Neman A Cire Shugaban INEC

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.