ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Ƙoli Kan Shari’ar Musulunci Ta Sake Neman A Cire Shugaban INEC

by Abubakar Sulaiman
5 months ago
Musulunci

Majalisar Ƙoli kan harkokin Shari’ar Musulunci a Nijeriya (SCSN) ta sake nanata kiranta na a cire Shugaban Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta (INEC), Farfesa Joash Amupitan, tana mai cewa ba ta da amincewa da cewa zai iya gudanar da zaɓe cikin adalci a babban zaɓen ƙasar da ke tafe.

Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da sakatare-janar na majalisar, Nafi’u Baba Ahmad, ya sanyawa hannu. Majalisar ta ce kiran da take yi ba shi da alaƙa da addini ko ƙabilanci, sai dai da batun nagarta da cancantar shugabanci. Ta bayyana cewa sabon bayanin ya zama dole ne bayan fassarar da aka yi wa wata sanarwa da ta fitar a baya ranar 28 ga Janairu.

  • Gudunmawar Shehu Ibrahim Inyass (RTA) Ga Musulunci A Wayewar Zamani (2)
  • Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko

Rahoton BBC ya bayyana cewa, Majalisar ta jaddada cewa ba a taɓa amfani da bambancin addini wajen amincewa ko ƙin amincewa da sakamakon zaɓe ba tun daga samun ’yancin kai a 1960. Ta ƙara da cewa daga shugabannin INEC 13 da suka gabata, Farfesa Attahiru Jega da Farfesa Mahmood Yakubu ne kaɗai musulmai, amma hakan bai taɓa haifar da ƙin amincewa da zaɓe daga musulman ƙasar ba.

ADVERTISEMENT

A cewar majalisar, dalilin neman cire Farfesa Amupitan ya shafi wasu abubuwan da ta ce ya aikata a baya, musamman wata takarda da ya jagoranci rubutawa a 2020, wadda a cikinta ta ce ya yi kalamai masu cin mutunci ga musulman Nijeriya, da Arewa da kuma Usman Ɗanfodio. Majalisar ta ce takardar ta yi zargin ana yi wa kiristoci “kisan kiyashi” tare da yunƙurin danganta matsalar tsaro da jihadin Ɗanfodio, abin da ta bayyana a matsayin kuskure kuma mai tayar da zaune tsaye.

Majalisar ta ƙara da cewa har zuwa yanzu Shugaban INEC bai fito ya nesanta kansa daga waɗannan kalamai ba, tana mai jaddada cewa shugabancin hukumar zaɓe na buƙatar mutum da ke kauce wa nuna bambancin addini ko ƙabilanci. A saboda haka, majalisar ta ce ba za ta amince da duk wani zaɓe da Farfesa Amupitan zai jagoranta ba.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Musulunci
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje
  • Abubakar Sulaiman
    Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Next Post
 ‘Yan Adawa Sun Sauya Sabuwar Dabarun Kifar Da Tinubu A 2027

 ‘Yan Adawa Sun Sauya Sabuwar Dabarun Kifar Da Tinubu A 2027

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.