Hukumar Hisbah shiyyar Katagum ta Jihar Bauchi ta kama mutane bakwai da ake zargi da gudanar da wata haramtacciyar al’ada ta musayar matan aure a ƙaramar hukumar Azare.
Kwamandan shiyyar, Malam Ridwan Muhammad Khairan, ya bayyana cewa an kama waɗanda ake zargin ne bayan koke-koken al’umma da kuma wasu mambobin ƙungiyar da ake kira Wuddadu. Ya ce mutanen na gudanar da wata hanya da ke ba su damar musayar matansu domin hulɗar aure da jima’i a tsakaninsu.
Ya jaddada cewa wannan ɗabi’a ba ta da tushe a addinin Musulunci, yana mai cewa waɗanda ke aikata hakan sun yi ƙoƙarin kare kansu da hujjar mafarki daga wani mamba, amma hakan ba ya da inganci a shari’a. Ya ƙara da cewa wannan aiki ya yi daidai da zina a ƙarƙashin dokokin Musulunci.
Hukumar ta ce rundunar “Operation Ko Ba Kobo” ce ta aiwatar da kamen bayan samun sahihan bayanai, inda waɗanda ake zargin suka amsa laifin aikata wannan abu ba tare da wani hujjar addini ba. An kuma gargaɗi al’umma da su guji irin wadannan dabi’u da suka saba wa koyarwar addini da al’ada.
Shugaban ƙungiyar Wuddadu a Azare, Malam Sagir Bashir, ya ce sun yi ƙoƙarin shawo kan lamarin ta hanyar nasiha da gargadi, amma abin ya ci gaba a boye, lamarin da ya sa suka kai ƙarar ga Hisba domin kare mutuncin al’umma. Ya tabbatar da cewa wannan dabi’a ba ta cikin koyarwar kungiyar.
Hukumar Hisba ta sake jaddada ƙudirinta na yaƙi da duk wata ɗabi’a da ta saɓa wa dokokin addini da zamantakewa, yayin da wadanda ake zargin suka nuna nadama tare da alkawarin daina aikata hakan, amma ana ci gaba da bincike domin ɗaukar matakin shari’a da ya dace.















Discussion about this post