A daren yau Laraba 6 ga watan Mayu, manyan ƙungiyoyin ƙwallon ƙafa na duniya, Bayern Munich da Paris Saint-Germain (PSG), za su kara a filin wasa na Allianz Arena da ke birnin Munich a ƙasar Germany, a wasan zagaye na biyu na kusa da na ƙarshe a gasar UEFA Champions League.
A wasan farko da aka buga a Paris makon da ya gabata, PSG ta doke Bayern Munich da ci 5-4, sakamakon da ya sa Bayern za ta shiga wasan yau da buƙatar juyar da akalar wasan domin samun gurbin zuwa wasan ƙarshe.
Duk ƙungiyar da ta yi nasara a wannan wasa za ta haɗu da Arsenal a wasan ƙarshe, bayan da Arsenal ta doke Atletico Madrid a wasan kusa da na ƙarshe da aka buga a ranar Talata.
A tarihi, ƙungiyoyin biyu sun haɗu sau 18, inda Bayern Munich ke da rinjaye da nasara 10, yayin da PSG ke da nasara 8. Wannan ya ƙara wa wasan armashi, musamman ga Bayern wadda ke neman ramuwar gayya a gida.
Ana sa ran wasan zai ƙayatar matuƙa, yayin da miliyoyin masoya ƙwallon ƙafa ke jiran ganin yadda za ta kaya a wannan fafatawa mai muhimmanci da za a buga da misalin ƙarfe 8 na dare agogon Nijeriya.















Discussion about this post